Ƴan asalin Najeriya 14 da za su buga kofin duniya a 2026
Super Eagles ba ta samu tikitin shiga gasar cin kofin duniya ta 2026 da za a fara daga ranar 11 ga watan Yuni ba a Amurka da Canada da kuma Mexico.
To sai dai tana da ƴan wasa 14 ƴan asalin Najeriya da za su wakilce ta da za a kara tsakanin kasashe 48 a karon farko a tarihin gasar.
Saboda haka, kasa shiga gasar da Najeriya ta yi ta bana, bai hanata samun ƴan ƙwallonta da za su wakilce ta a babbar gasar tamaula ta duniya.
Kenan Najeriya tana da wakilci na daban a gasar—wanda ba a kan sunan ƙasa kai tsaye bane—amma ta hanyar ƴan ƙwallo fiye da 14 masu asalin Najeriya da za su wakilci ƙasashe takwas daban-daban a gasar da za a gudanar.