Ba za mu yi sulhu da ƴanbindiga a Arewa Maso Yamma ba - Gwamnan Sokoto

Asalin hoton, Ahmad Aliyu
Gwamnan jihar Sokoto, Ahmed Aliyu, ya ce gwamnonin arewa maso yammacin Najeriya ba za su yi sulhu da ƴanbindigar da ke addabar yankin ba.
Yayin da yake jawabi a wurin bikin ƙaddamar da wani titi da gwamnan Katsina ya gina, Ahmad Aliyu ya ce gwamnonin yankin na yin aiki tare domin kawo ƙarshen matsalar.
Yankin arewa maso yammacin Najeriya dai ya shafe shekaru yana fuskantar hare-haren ƴanfashin daji, masu garkuwa da mutane domin neman kuɗin fansa, lamarin da ya sa ake tsananta kiraye-kirayen kawo ƙarshen matsalar, ciki har da masu kiran amfani da hanyar sulhu.
Sai dai gwamnan na Sokoto ya ce ba za su yi tattaunawar sulhu da ƴanbindigar ba.
“Ba za mu yi sulhu da kowane mai laifi ba, ba za mu amince da duk wata buƙatarsu ba, har sai sun amince za su ajiye makamansu ba tare da kowane irin sharaɗi ba,'' kamar yadda ya jaddada.
Gwamnan ya ci gaba da cewa gwamnatocin jihohin yankin na aiki da jami'an tsaro don kawo ƙarshen matsalar.
Ya kuma yi kira ga mutane su riƙa bai wa gwamnati da jami'an tsaro haɗin kai wajen fallasa masu kwarmata wa ƴanbingar bayanan sirri, yana mai cewa babu wani harin, yanbindiga da zai gudana ba tare da hadin bakin ƴan garin ba.



