KAI TSAYE, Yaƙin Iran da abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sassan duniya

Wannan shafi ne da ke kawo muku irin wainar da ake toyawa a yaƙin da Amurka da Isra'ila ke yi a kan Iran da sauran abubuwan da ke faruwa a sassan duniya na ranar 27/04/2026

Rahoto kai-tsaye

Ibrahim Haruna Kakangi da Aisha Aliyu Jaafar da Abdullahi Bello Diginza

  1. Buƙatun Amurka na son kai ne suka sa aka gaza cimma matsaya - Iran

    Abbas Aragchi

    Asalin hoton, Getty Images

    Bayanan hoto, Ministan harkokin waje na Iran Abbas Aragchi

    Ministan harkokin wajen Iran Abbas Araqchi, ya ce an gaza cimma matsaya a tattaunawar da suka yi da Amurka a farkon wannan watan da nufin kawo karshen yaƙin ne saboda abin da ya kira '' buƙatun Washington na son rai".

    A yayin da ya isa Rasha domin tattaunawa da shugaba Putin, Mista Arachi ya ce tattaunawar zaman lafiyar zagaye na farko a Pakistan ya soma samun nasara, amma kuma daga bisani ya ruguje saboda yadda Amurka ta tunkari tattaunawar.

    Kafafen yaɗa labarai na Amurka sun ruwaito cewa Iran ta gabatar da wani sabon ƙuduri ga Washington na yadda za a buɗe mashigar Hormuz da kuma kawo ƙarshen yaƙin, amma kuma ta ɗage batun tattaunawa kan nukiliya zuwa wani lokaci na gaba.

  2. Gwamnatin Nijar ta haramta sayar da shinkafar Bulmex

    shikafa a hannu da ake ɗibo daga buhu

    Asalin hoton, Getty Images

    Ma’aikatar kasuwanci a Jamhuriyar Nijar ta haramta sayar da wata shinkafa da ake kira Bulmex.

    Gwamnatin ta hana shigowa da sayar da wannan shinkafa a faɗin ƙasar, sakamakon wani sinadari mai cutarwa da aka ce bincike ya gano a cikinta.

    A cikin wata sanarwa da gwamnatin ta fitar mai lamba 0031, ma'aikatar ta ce bayan binciken lafiya da aka yi a kasuwanni, an gano ɓurɓushin ƙarfe a wasu buhuhunan shinkafar.

    Sanarwar ta kuma yi kira ga yan kasuwa su yi gaggawar fitar da shinkafar daga shagunansu ko su fusknaci hukunci.

    Mamman Nouri, shugaban wata kungiyar kare masu sayen kaya a Nijar, ya yabawa matakin gwamnati, sai dai ya kuma ce akwai sakaci daga bangaren gwamnati na rashin yin binciken da ya dace kan abubuwan da ake shigarwa ƙasar.

    Mamman ya kuma yi kira ga ƴan kasuwa su yi hattara tare da yin taka-tsantsan kan wasu dabaru da yake zargi ana yi don shigar da shinkafar, '' zai iya yiwuwa a chanza mata buhu, don haka in ka siya ta buɗe, in akwai mayen karfe ka saka, zai janyo duk wani karfe da ke ciki, idan an samu, daga nan sai ka gaya wa hukuma mafi kusa'' in ji shi.

  3. Rikicin ƙabilanci ya yi sanadin mutuwar mutum fiye da 40 a gabashin Chadi

    Jami’an gwamnati a ƙasar Chadi, sun ce aƙalla mutane arba’in da biyu ne suka mutu a wani rikici da ya ɓarke tsakanin ƙabilu a gabashin ƙasar.

    An yi imanin cewa tashin hankalin da ya faru a lardin Wadi Fira, ya samo asali ne daga taƙaddama kan wata rijiyar ruwa, lamarin da daga bisani ya haifar da jerin hare haren ramuwar gayya a faɗin yankin.

    Mataimakin firaministan ƙasar, Limane Mahamat, ya shaida wa gidan talabijin ɗin ƙasar cewa yanzu an shawo kan lamarin.

    Gabashin Chadi dai ya daɗe yana fama da rikice-rikicen kabilanci tsakanin manoma da larabawa makiyaya tsawon shekaru.

    Sai dai kuma rikicin ya ƙara tsananta sakamakon ƙarancin albarkatu da matsalolin tsaro, musamman bayan kwararar ‘yan gudun hijira sakamaon yaƙin basasar Sudan.

  4. Yau za a gurfanar da mutumin da ake zargi da kai wa Trump hari

    wani mutum a kwance da hannunsa a baya

    Asalin hoton, @REALDONALD TRUMP / TRUTHSOCIAL

    Nan gaba a yau Litinin ne za a gurfanar da mutumin da ake zargi da kutsawa wajen wata liyafar cin abinci domin kai hari ga Shugaban Amurka, Donald Trump.

    Za a tuhumi Cole Tomas, mai shekara 31 a duniya, daga Los Angeles, da laifin kai hari ga jami’in gwamnatin tarayya da kuma amfani da bindiga yayin aikata laifin.

    Ana zargin ya buɗe wuta ne a kusa da wurin binciken jami'an tsaro, lamarin da ya tilasta fitar da Shugaba Trump daga wurin cikin gaggawa.

    Jami’an tsaro sun ce an samu wani sakon email da maharin ya aikawawa 'yan uwansa mintuna kaɗan kafin ƙaddamar da harin, inda a ciki yake bayani a kan ajandarsa ta kai hari kan jami'an gwamnatin Mista Trump din.

  5. Ƴan bindiga sun kashe Ministan tsaron Mali Sadio Camara

    Sadio Camara

    Asalin hoton, Reuters

    Ministan tsaron Mali, Sadio Camara, ya rasu sakamakon wani harin ƙunar baƙin wake da aka kai gidansa da ke kusa da babban birnin ƙasar, Bamako, a ranar Asabar.

    Harin na ɗaya daga cikin jerin hare-hare da masu ɗauke da makamai da kuma ‘yan awaren Tuareg suka kai a wasu birane daban-daban a lokaci guda.

    Wakilin BBC ya ce tsawon gwamman shekaru kenan ƴan awaren na Tuareg da a aka fi sani da FLA ke ta ƙokarin ɓallewa don kafa na su shugabancin, a wannan yanki, lamarin da ya sa suka haɗa kai da ƙungiyar JNIM mai akala da Alqa'eda wadda ita kuma manufarta ita ce yana manufarta a yankin wajen kai waɗannan hare hare.

    A yanzu dai ƴan tawayen na Tuareg sun ce suna riƙe da garin Kidan, mai muhimmanci na yankin hamada, inda wata rundunar tsaron Rasha ke da sansani.

    Haka kuma an kai hari gidan shugaban mulkin sojin kasar Assimi Goïta, amma bai samu wani rauni ba.

  6. Wakilin Iran ya isa Rasha domin ganawa da Putin

    Araqchi na gaisawa da jami'an Rasha

    Asalin hoton, TELEGRAM/REUTERS

    Ministan harkokin wajen Iran, Abbas Araghchi, ya isa birnin St Petersburg domin tattaunawa da shugaban Rasha, Vladimir Putin.

    Rahotannin kafafen watsa labaran Amurka sun ce Iran ta gabatar da wani sabon shiri ga Washington, wanda ya mayar da hankali kan buɗe mashigin Hormuz, da kuma kawo ƙarshen yaƙin, wanda kuma ya buƙaci ɗage tattaunawar nukiliya zuwa wani lokaci na gaba.

    Tun da farko, Mista Araghchi ya ce tattaunawarsa a ƙasar Oman a ranar Lahadi ta mayar da hankali kan hanyoyin tabbatar da zirga-zirgar jiragen ruwa ta mashigin.

    Sai dai Shugaba Donald Trump ya ce dole ne duk wata yarjejeniya ta ƙunshi buƙatar Iran ta yi watsi da duk wani yunƙuri na ƙera makamin nukiliya.

  7. Buɗewa

    Masu bin shafin BBC Hausa kai-tsaye barkanmu da shiga sabon mako.

    A yau Litinin ma mun shirya tsaf domin kawo muku labarai kan halin da duniya ke ciki.

    Ku biyo mu a shafukanmu na sada zumunta domin tafka muhawara kan labaran da muke wallafawa, har ma ku kalli bidiyon da muka wallafa.