Kana amfani da shafin BBC mai bayyana rubutu kawai (babu hoto) domin rage cin data. Idan ana so a ga hotuna da bidiyo sai a koma babban shafinmu.

Koma shafi mai hoto

Samu ƙarin bayani kan shafin tattalin data

KAI TSAYE, Abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya

Wannan shafi ne na kai tsaye da ke kawo muku labaran abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya a ranar Talata 15/09/2026

Taƙaitattu

Rahoto kai-tsaye

Nabeela Mukhtar Uba da Usman Minjibir

  1. Gwamnatin Sokoto ta rufe masallacin Sheikh Musa Lukuwa

    Gwamnatin Jihar Sokoto ta sanar da rufe masallacin Juma’a na Musa Lukuwa har sai yadda hali ya yi bayan tashin hankalin da ya faru a makon da ya gabata inda wani matashi ya daɓawa malamin wuƙa.

    Cikin wata sanarwa da Daraktan yada labarai na gwamnatin Sokoto, Abubakar Bawa, ya fitar, gwamnatin ta ce ta ɗauki matakin ne domin bayar da damar yin bincike kan harin da aka kai tare da kisa.

    Sanarwar ta kuma ce gwamnati ta kafa kwamitin malamai domin gudanar da bincike kan musabbabin rikicin inda kuma ake sa ran kwamitin zai bai wa gwamnati shawarwari kan matakan da suka dace a ɗauka.

    Gwamnatin ta kuma nesata kanta daga duk wani al'amari na fakewa da addini don yin ɓatanci ga fiyayyen halitta Annabi Muhammad SAW.

    Sanarwar ta yi kira ga al’ummar jihar da su guji furta kalamai masu tayar da hankali da ka iya tunzura jama’a da kawo cikas ga zaman lafiya da haɗin kan al'ummar jihar.

    Malam Musa Ayuba Lukuwa malamin addinin Musulunci ne a jihar Sokoto da ke bin fahimtar Ahlussunnah Wal Jama'a.

    Yana daga cikin malamai masu yawan janyo taƙaddama musamman dangane da al'amura masu sarƙaƙiya.

  2. Ana ci gaba da yaƙi tsakanin Houthi da Saudiyya

    Ana ci gaba da gwabza faɗa tsakanin 'yan tawayen Houthi a Yemen da kuma Saudiyya, inda ɓangarorin biyu ke bayar da rahoton ƙarin asarar rayuka da jikkatar da aka samu.

    Ƙawancen sojojin da Saudiyya ke jagoranta, wanda ke marawa gwamnatin Yemen baya, ya ce mutum 13 fararen hula sun jikkata sakamakon hare-haren makamai masu linzami da jirage marasa matuƙi da mayakan Houthi suka kai kan biranen Khamis Mushait, da Abha da kuma Taif da ke kudancin Saudiyya.

    A Yemen kuma, kafar yaɗa labaran 'yan Houthi ta ruwaito cewa mutum uku sun mutu a hare-haren sama da rundunar ƙawancen da Saudiyya ke jagoranta ta kai a lardin Taiz da ke kudu maso yammacin ƙasar.

    Tun da farko a ranar Litinin, mayakan na Houthi sun kai hari kan sansanin sojin sama na Sarki Khalid da ke kudancin Saudiyya.

    Wakilin BBC ya ce ƙara ta'azzarar da rikicin ke yi ya ƙara sanya damuwa a kan batun samar da makamashi da kuma batun tsaron jiragen ruwa.

  3. Ba ma yaƙi da Saudiyya - Iran

    Shugaban Iran, Massoud Pezeshkian ya ce ƙasarsa ba yaƙi take da Saudiyya ba inda ya ce ƙasashen Gabas ta Tsakiya ba su fahimci dalilan hare-haren da Iran ɗin ke kai wa sansanonin sojojin Amurka a yankin ba.

    A hirar da ya yi da kafar yaɗa labarai ta India Today yayin da ya halarci taron BRICS, Mr Pezeshkian y ace “ba ma yaƙi da Saudiyya sannan suma ƴan Houthi suna da nasu matsalolin. Ya kamata duka ƙasashen yankin su zauna domin tattauna hanyoyin samar da zaman lafiya da tsaro. Babu wani dalili na yaƙar junanmu.”

    Shugaban na Iran ya kuma jaddada cewa “matsalar it ace Amurka ta kafa sansanin soji a ƙasashen Larabawa. Suna kai mana hare-hare daga sansanonin.”

    “Ba zai yiwu a ci gaba da kai mana hare-hare daga wuri guda ba a kullum”, kamar yadda Mr Pezeshkian ya bayyana.

  4. Karatu don nishaɗi na da alaƙa da ingantacciyar lafiyar ƙwaƙwalwa - Bincike

    Masu bincike a Birtaniya sun gano cewa yin karatu don nishaɗi na da alaƙa da samun ingantacciyar lafiyar ƙwaƙwalwa, da rage damuwa da kuma rage yiwuwar kamuwa da cutar mantuwa.

    A cikin wani sabon nazari da suka yi bayan tattara hujjoji da dama ciki har da takardun bincike, da sakamakon binciken jin ra’ayin jama’a da kuma hotunan binciken ƙwaƙwalwa, masana kimiyyar daga Jami’ar Cambridge sun bayyana cewa yin karatu akai-akai, ko da kuwa wane irin littafi ne, na iya samar da fa’idojin lafiya a kowanne mataki na rayuwa.

    Ɗaya daga cikin sakamakon binciken, wanda ya shafi matasa sama da dubu goma, ya nuna cewa waɗanda suka fara karatu don nishaɗi tun suna ƙanana, sun fi kwakwalwa sosai da mayar da hankali a kan karatu.

    Binciken ya kuma nuna cewa irin waɗannan matasa sun fi samun nasara a makaranta, idan aka kwatanta da takwarorinsu da ba sa yawan karatu don nishaɗi.

  5. Isra'ila ta sanar da mutuwar kwamandan sojin Hamas a Gaza

    Rundunar sojin Isra'ila ta sanar da mutuwar wani kwamandan sojin Hamas a Gaza.

    Ita ma kafar yaɗa labarai ta Falasɗinu ta tabbatar da mutuwar Ahmed al-Batash, da aka fi sani da "Abu Osama".

    Kafar yaɗa labaran ta ce harin da aka kai ta sama ya shafi motarsa.

    An tsara cewa Mohammed bin Salman zai gana da Shugaban Masar Abdel Fattah al-Sisi nan da sa'oi masu zuwa.

    Lamarin na zuwa ne yayin da ƴan Houthi suka yi iƙirarin ci gaba da kai hare-hare kan wasu cibiyoyi a Saudiyya.

    Mohsen Rezaei, Sakataren babban Majalisar tsaron Iran ya sake nanata cewa Tehran ba za ta tattauna da Amurka ba har sai an biya buƙatun da aka gabatar a yarjejeniyar fahimta da aka gabatar.

  6. Maraba

    Barkan ku da zuwa shafin Kai Tsaye na BBC Hausa da ke kawo muku labarai na abubuwan da ke faruwa a Najeriya da ma sauran sassan duniya.

    Sai ku kasance tare da mu a wannan rana ta Talata don sanin halin da ƙasashen duniya ke ciki.

    Sunana Nabeela Mukhtar Uba kuma zan kasance da ku har zuwa anjima da abokan aiki za su karɓi ragama.

    Kuna iya leƙawa shafukanmu na sada zumunta domin samun ƙarin labarai har ma da kallon bidiyo.