KAI TSAYE, Abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya

Wannan shafi ne na kai tsaye da ke kawo muku labaran abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya a ranar Talata 15/09/2026

Taƙaitattu

Tsallake Bidiyo ka ci gaba
  • Hoto
  • Cyber Truck
  • Adeyemi Adeniyi
  • Abdourahamane Tchiani
  • Atiku Abubakar
  • NFF
  • Badriyyah Tijjani Kalarawi
  • Ranar Hausa: BBC
  • Danjuma Goje
  • Zainab
  • BBC
  • ABU
  • xxx
  • xxx
  • Khalifa Dokaji
  • Sheikh Jingir

Rahoto kai-tsaye

Nabeela Mukhtar Uba da Usman Minjibir

  1. Karatu don nishaɗi na da alaƙa da ingantacciyar lafiyar ƙwaƙwalwa - Bincike

    Karatu

    Asalin hoton, Getty Images

    Masu bincike a Birtaniya sun gano cewa yin karatu don nishaɗi na da alaƙa da samun ingantacciyar lafiyar ƙwaƙwalwa, da rage damuwa da kuma rage yiwuwar kamuwa da cutar mantuwa.

    A cikin wani sabon nazari da suka yi bayan tattara hujjoji da dama ciki har da takardun bincike, da sakamakon binciken jin ra’ayin jama’a da kuma hotunan binciken ƙwaƙwalwa, masana kimiyyar daga Jami’ar Cambridge sun bayyana cewa yin karatu akai-akai, ko da kuwa wane irin littafi ne, na iya samar da fa’idojin lafiya a kowanne mataki na rayuwa.

    Ɗaya daga cikin sakamakon binciken, wanda ya shafi matasa sama da dubu goma, ya nuna cewa waɗanda suka fara karatu don nishaɗi tun suna ƙanana, sun fi kwakwalwa sosai da mayar da hankali a kan karatu.

    Binciken ya kuma nuna cewa irin waɗannan matasa sun fi samun nasara a makaranta, idan aka kwatanta da takwarorinsu da ba sa yawan karatu don nishaɗi.

  2. Isra'ila ta sanar da mutuwar kwamandan sojin Hamas a Gaza

    Hamas

    Asalin hoton, Ayman Majed Harb Alhisi/Anadolu via Getty Images

    Rundunar sojin Isra'ila ta sanar da mutuwar wani kwamandan sojin Hamas a Gaza.

    Ita ma kafar yaɗa labarai ta Falasɗinu ta tabbatar da mutuwar Ahmed al-Batash, da aka fi sani da "Abu Osama".

    Kafar yaɗa labaran ta ce harin da aka kai ta sama ya shafi motarsa.

    An tsara cewa Mohammed bin Salman zai gana da Shugaban Masar Abdel Fattah al-Sisi nan da sa'oi masu zuwa.

    Lamarin na zuwa ne yayin da ƴan Houthi suka yi iƙirarin ci gaba da kai hare-hare kan wasu cibiyoyi a Saudiyya.

    Mohsen Rezaei, Sakataren babban Majalisar tsaron Iran ya sake nanata cewa Tehran ba za ta tattauna da Amurka ba har sai an biya buƙatun da aka gabatar a yarjejeniyar fahimta da aka gabatar.

  3. Maraba

    Barkan ku da zuwa shafin Kai Tsaye na BBC Hausa da ke kawo muku labarai na abubuwan da ke faruwa a Najeriya da ma sauran sassan duniya.

    Sai ku kasance tare da mu a wannan rana ta Talata don sanin halin da ƙasashen duniya ke ciki.

    Sunana Nabeela Mukhtar Uba kuma zan kasance da ku har zuwa anjima da abokan aiki za su karɓi ragama.

    Kuna iya leƙawa shafukanmu na sada zumunta domin samun ƙarin labarai har ma da kallon bidiyo.