KAI TSAYE, Yaƙin Iran da sauran abubuwan da ke faruwa a sassan duniya

Wannan shafi ne da ke kawo muku labaran yaƙin Iran da sauran abubuwan da ke faruwa a sassan duniya, Litinin 04/05/2026

Rahoto kai-tsaye

Haruna Ibrahim Kakangi da Aisha Aliyu Jaafar

  1. Mutum 5,000 sun tsere daga gidanjensu a Philippines bayan aman wuta da wani dutse ya yi

    dutse mai aman suta

    Asalin hoton, Marco Restivo / Barcroft Media

    Dubban mutane a Philippines sun tsere daga gidajensu sakamakon aman wuta da wani dutse ya yi a kasar.

    Dutsen Mayon da ke yankin Bicol ya yi aman ne ranar Asabar din da ta gabata, inda ya fitar da toka da ta turnuƙe sararin samaniya.

    Sama da mutane dubu biyar da ke zaune a kasan dutsen yanzu haka suna matsugunan gaggawa na wucin gadi, yayin da hukumomi ke kokarin bude hanyoyin da toka ta mamaye.

    Kasar Philippines na daya daga cikin kasashen da suka fi fuskantar bala'i a duniya, inda ake yawan samun duwatsu masu aman wuta da girgizar kasa da ambaliya da kuma zabtarewar kasa.

  2. Za a gudanar da azumi a Nijar domin neman nasara a yaƙi da ƴan bindiga

    mace na addu'a da charbi a hannu

    Asalin hoton, Getty Images

    A jamhuriyar Nijar, a yau Litinin ne gwamnatin mulkin sojan ƙasar ta ware domin gudanar da azumi a faɗin ƙasar.

    Zaman majalisar ministoci na ƙarshen mako ne ya umurci al'ummar ƙasar da su gudanar da azumin na yau tare da addu'o'in Allah ya ba ƙasashen AES nasara a yaƙin da suke yi da ƙungiyoyi masu ɗauke da makamai.

    Yanayin tsaro a yankin Sahel na ci gaba taɓarɓarewa yayin da masu iƙirarin jihadi ke ƙara matsa lamba kan sojojin ƙasashen.

    Ƙasashen uku da suka haɗa da Nijar da Mali da Burkina Faso na ƙara fuskantar matsala wajen aiwatar da iko a kan dukkanin yankunansu, har ma ya kai wasu yankuna sun faɗa hannun ƴan bindigar.

    Lamarin ya sake ta'azzara ne bayan harin haɗin gwiwar da masu iƙirarin jihadi suka kai a Mali a ƙarshen watan da ya gabata.

    A jamhuriyar NIjar, bayan matakan sojin da gwamnatin mulkin soji ta ce tana ɗauka a yayin zaman majalisar a ƙarshen mako, ta kuma buƙaci ƴan ƙasar da su duƙufa yin addu'oi domin nasara a kan abokan gaba

    Wasu ƴan ƙasar dai sun bayyana ra'ayoyinsu inda suka ce suna fatan azumin ya zama karɓaɓɓe, inda wasu suka ce dama sukan yi azumin, kuma idan hakan bai saɓawa addini ba za su yi.

  3. Amurka za ta miƙa wa Iran ma'aikatan jirgin ruwan da ta kama a watan da ya gabata

    jirgin ruwan sojin Amurka yayin da ya kai hari kan wani jirgin ruwan Iran

    Asalin hoton, Centcom

    Gwamnatin Pakistan ta ce Amurka ta miƙa mata ma'aikata 22 dake cikin jirgin ruwan Iran da ta kama a watan da ya gabata, kuma nan gaba a yau za ta miƙa su ga hukumomi a Iran.

    Dakarun Amurka sun ƙwace jirgin na Touska a watan da ya gabata, bayan sun kai hari kan ɗakin da injinsa yake.

    Iran ta bayyana kama jirgin a matsayin 'fashin teku', yayin da Shugaba Trump kuma ya ce 'jirgin yayi ƙoƙarin tsallake shingen da sojojin ruwan Amurka suka sanya ne'.

    Pakistan ta ce mayar da ma'aikatan jirgin wani mataki ne na Amurka na samar da ƙwarin gwiwa a ƙoƙarin da ake na samar da sasanci tsakaninsu.

    Ta kuma ce za a kai jirgin ruwa kan tekun yankin Pakistan, kuma za a mayar wa masu shi da zarar an kammalla gyara shi.

  4. Najeriya za ta kwaso ƴan ƙasarta da ke son komawa gida daga Afirka ta Kudu

    masu zanga zanga a Afirka ta Kudu

    Asalin hoton, KIM LUDBROOK/EPA/Shutterstock

    Najeriya ta soma shirin dawo da ƴan ƙasarta da ke son komawa gida daga Afirka ta Kudu, a yayin da ake samun ƙaruwar fargaba cewa za a iya samun ƙaruwar kai hari kan baƙi.

    Ministar harkokin wajen ƙasar Bianca Odumegwu-Ojukwu ta ce zuwa yanzu mutum 130 sun yi rijista cikin shirin, inda ta ce ana hasashen adadin zai ƙaru.

    A cikin sanarwar da ta fitar, ta bayyana irin damuwar da shugaban ƙasar Bola Ahmed Tinubu ya yi kan hare haren da ake kai wa a ƙasar, kuma ya yi Allah wadai da tashin hankali da kuma zanga zangar ƙin jinin baƙi da kuma kalaman nuna ƙiyayya da masu zanga zangar ke yi.

    Ministar ta kuma ce an kashe ƴan Najeriya biyu a hare hare daban daban wanda jami'an tsaro suka yi, inda ta jaddada cewa ƙasarta na neman adalci.

    Shugaban Afirka ta Kudun Cyril Ramaphosa ya yi Allahwadai da hare haren, sai dai kuma ya gargaɗi ƴan ƙasashen wajen da ke ƙasar da su mutunta dokokin ƙasar.

  5. Wata babbar mota ta auka cikin jama'a a filin wasan motoci a Colombia

    babbar mota

    Asalin hoton, Popaya Pauta Via Facebook

    Mutane 3 sun mutu, yayin da wasu fiye da talatin suka samu raunuka lokacin da wata babbar mota ta auka cikin jama'a a wani filin wasan motoci a ƙasar Colombia.

    Lamarin ya faru ne a Popayán da ke yankin kudancin jihar Cauca.

    Ƴan sanda sun shaida wa kafafen yaɗa labarai na cikin gida cewa birkin motar ne ya samu matsala.

    Wakilin BBC ya ce wani bidiyo mai tayar da hankali da ƴan kallo suka naɗa ya nuna yadda motar ta tsallaka shingen da ya kyallace ƴan kallo daga filin wasan ta kuma auka cikin mutane.

    Gwamnan jihar Cauca, Octavio Guzmán, ya jajantawa waɗanda abin ya shafa, ya kuma ce an umarci asibitocin yankin da su kula da waɗanda suka ji rauni.

  6. Za mu kai hari kan dakarun Amurka idan suka bi ta Mashigar Hormuz - Iran

    jiragen ruwa

    Asalin hoton, Reuters

    Bayanan hoto, Jiragen ruwa a Mashigar Hormuz, an ɗauki hoton daga gaɓar Oman a ranar 1 ga watan Mayu

    Rundunar sojin Iran ta ce za ta kai hari kan dakarun Amurka idan har suka shiga Mashigar Hormuz - bayan da shugaba Trump ya ce Rundunar sojin Amurka za ta fara raka jiragen ruwan ƴan kasuwa da za su wuce ta Mashigar Hormuz, a yau litinin

    Sanarwar ta ce shirin, wanda Mista Trump ya yi wa laƙabi da Project Freedom, zai kunshi dakarun sojin Amurka dubu goma sha biyar, da jiragen ruwan yaƙi masu lalata makamai masu linzami da kuma jiragen saman yaƙi sama da ɗari.

    Wakilin BBC ya ce shugaban ya ce Amurka za ta raka waɗannan jiragen ruwan su fice daga yankin, kuma za zu ci gaba da gudanar da kasuwancinsu ba tare da wata matsala ba.

    Tun da farko dai, Wani babban jami'in Iran Ebrahim Azizihas ya yi gargadin cewa za a ɗauki duk wani yunƙurin Amurka na yin katsalandan a harkokin mashigar ruwan a matsayin keta yarjejeniyar tsagaita wuta da aka cimma.

  7. Buɗewa

    Masu bin shafin BBC Hausa kai-tsaye barkanmu da shiga sabon mako.

    A yau ma, kamar yadda muka saba, za mu kawo muku labaran irin wainar da ake toyawa a sassan duniya, kama daga yaƙin Amurka da Isra'ila kan Iran, da abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran ƙasashen Afirka.

    Muna fatan za ku kasance tare da mu.