KAI TSAYE, Abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya 29/8/2026

Wannan shafi ne da ke kawo muku abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya na ranar Asabar 29 ga watan Agustan 2026.

Tsallake Bidiyo ka ci gaba
  • Atiku Abubakar
  • NFF
  • Badriyyah Tijjani Kalarawi
  • Ranar Hausa: BBC
  • Danjuma Goje
  • Zainab
  • BBC
  • ABU
  • xxx
  • xxx
  • Khalifa Dokaji
  • Sheikh Jingir
  • Kano
  • Seriki Abbas
  • xxx

Rahoto kai-tsaye

Daga Aisha Babangida da Isiyaku Muhammed

  1. Iran ta ce za ta kai hari kan dukkan wuraren Amurka idan yaƙi ya ci gaba

    .....

    Asalin hoton, Getty Images

    Iran ta yi gargaɗin cewa za ta kai hare-hare kan dukkan sansanonin soja da sauran wuraren Amurka da ke yankin Gabas ta Tsakiya idan yaƙin da ake yi ya ci gaba.

    Ministan Harkokin Wajen Iran, Abbas Araqchi, ya ce Tehran ta riga ta sanar da ƙasashen yankin cewa duk wani hari da Amurka ta kai wa Iran zai fuskanci martani kai tsaye kan muradun Amurka a yankin.

    Ya kuma bayyana hare-haren da Amurka da Isra'ila suka kai Iran ba bisa ka'ida bane, yayin da ya ce Iran za ta mayar da martani ne domin kare kanta.

    Araqchi ya ce makamai masu linzamin Iran sun nuna ƙarfinsu a yaƙin baya-bayan nan, yana mai iƙirarin cewa Amurka da Isra'ila sun kasa dakile su yadda ya kamata.

    Haka kuma ya ce Iran na son inganta dangantaka da ƙasashen Musulmi da maƙwabtanta, ciki har da Masar da Lebanon.

  2. Amurka ta samu iko da fiye da rabin man fetur ɗin Venezuela - Trump

    ....

    Asalin hoton, Getty Images

    Shugaban Amurka Donald Trump ya yi iƙirarin cewa Amurka ta samu iko da fiye da rabin arzikin man fetur na Venezuela, yana mai cewa hakan ya ƙarfafa tasirin Washington a fannin makamashi a yankin.

    Trump ya bayyana haka ne yayin da ake ci gaba da tattaunawa kan manufofin makamashi da dangantakar Amurka da ƙasashen Latin Amurka.

    Sai dai bai yi cikakken bayani kan yadda Amurka ta samu wannan iko ba.

    Venezuela na ɗaya daga cikin kasashen masu manyan arzikin man fetur a duniya, kuma albarkatun makamashinta na ci gaba da kasancewa muhimmin batu a siyasa da tattalin arzikin duniya.

  3. Iran ta ce tana da wadataccen mai da zai samar mata kuɗaɗen kasafi

    ...

    Asalin hoton, Tasnim news agency

    Iran ta ce tana da isasshen man fetur da za ta sayar domin samar da kuɗaɗen da ake buƙata a kasafin kuɗinta duk da toshe tasoshin ruwanta da Amurka ta yi kamar yadda kamfanin dillanacin labaran Fars ya ruwaito.

    Fars ya ce ma’aikatar man tetur ta ƙasar ta ce kuɗaɗen da aka samu daga man fetur a watanni huɗun farko na shekarar nan sun kai kashi 99 cikin 100 na abin da aka tsara a kasafin kuɗi.

    Haka kuma, ma’aikatar ta ce ta tura dala biliyan 7.5 da aka samu daga sayar da man fetur zuwa Babban Bankin Iran a cikin watanni huɗun farko na shekarar, kuma ana sa ran kuɗaɗen za su taimaka wajen biyan buƙatun kuɗaɗen musayar ƙasashen waje na gwamnati daga watan Afrilu zuwa Janairu.

  4. Assalamu alaikum!

    Jama'a barkanmu da wannan safiya ta Asabar daga wannan shafin namu na BBC Hausa, inda za mu ci gaba da kawo muku labaran kai-tsaye na abubuwan da suke faruwa a Najeriya da sassan duniya.

    Aisha Babangida ce za ta kasance da ku daga yanzu zuwa yamma.

    Za ku iya leƙawa shafukanmu na sada zumunta na facebook da X da kuma whatsapp domin karanta wasu labaran da kallon bidiyo da ma tafka muhawara.

    Ku kasance tare da mu.