Iran ta ce za ta kai hari kan dukkan wuraren Amurka idan yaƙi ya ci gaba

Asalin hoton, Getty Images
Iran ta yi gargaɗin cewa za ta kai hare-hare kan dukkan sansanonin soja da sauran wuraren Amurka da ke yankin Gabas ta Tsakiya idan yaƙin da ake yi ya ci gaba.
Ministan Harkokin Wajen Iran, Abbas Araqchi, ya ce Tehran ta riga ta sanar da ƙasashen yankin cewa duk wani hari da Amurka ta kai wa Iran zai fuskanci martani kai tsaye kan muradun Amurka a yankin.
Ya kuma bayyana hare-haren da Amurka da Isra'ila suka kai Iran ba bisa ka'ida bane, yayin da ya ce Iran za ta mayar da martani ne domin kare kanta.
Araqchi ya ce makamai masu linzamin Iran sun nuna ƙarfinsu a yaƙin baya-bayan nan, yana mai iƙirarin cewa Amurka da Isra'ila sun kasa dakile su yadda ya kamata.
Haka kuma ya ce Iran na son inganta dangantaka da ƙasashen Musulmi da maƙwabtanta, ciki har da Masar da Lebanon.

















