An saki Turawa mata biyu da aka yi garkuwa da su a Nijar
Wata ƴar ƙasar Austria da wata ƴar ƙasar Switzerland da aka yi garkuwa da su a lokuta daban-daban a arewacin Nijar a shekarar 2025, sun shaƙi iskar ƴanci, kamar yadda kamfanin dillancin labarai mai zaman kansa na Air Info Agadez ya ruwaito a ranar 11 ga Satumba.
Sai dai har zuwa yanzu babu wata sanarwa a hukumance da ta tabbatar da sakin Eva Gretzmacher, ƴar Austria, da Claudia Abbt, ƴar Switzerland.
An yi garkuwa da matan biyu ne daga gidajensu a Agadez a watan Janairu da Afrilu na 2025, yayin da wasu majiyoyi suka danganta sace su da ƙungiyar IS.
Rahoton ya ce tun bayan da aka yi garkuwa da su, an yi ƙoƙarin ganin an sake su, amma ba a samu nasara ba.
Wani ɗan uwan ɗaya daga cikin matan da aka yi garkuwa da su ya shaida wa Air Info Agadez cewa ba su da wani cikakken bayani da ke tabbatar da sakin ta, duk da cewa sun shafe kwanaki suna jiran samun labari mai daɗi.
Abbt ta shafe shekaru da dama tana zaune a Agadez tare da mijinta ɗan Nijar. Babu wata ƙungiya da ta fito ta ɗauki alhakin sace ta.
Gretzmacher, mai shekara 73, ta shafe shekara 28 tana zaune a Agadez kafin a yi garkuwa da ita. Ita ce ta kafa ƙungiyar Amanay, kuma ta kasance mai ruwa da tsaki a ayyukan da suka shafi ilimi da ƙarfafa mata da kare muhalli da al'adu da fasaha.