Kana amfani da shafin BBC mai bayyana rubutu kawai (babu hoto) domin rage cin data. Idan ana so a ga hotuna da bidiyo sai a koma babban shafinmu.

Koma shafi mai hoto

Samu ƙarin bayani kan shafin tattalin data

KAI TSAYE, Abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya

Wannan shafi ne na kai tsaye da ke kawo muku labaran abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya a ranar Juma'a 11/09/2026

Rahoto kai-tsaye

Isiyaku Muhammed

  1. An saki Turawa mata biyu da aka yi garkuwa da su a Nijar

    Wata ƴar ƙasar Austria da wata ƴar ƙasar Switzerland da aka yi garkuwa da su a lokuta daban-daban a arewacin Nijar a shekarar 2025, sun shaƙi iskar ƴanci, kamar yadda kamfanin dillancin labarai mai zaman kansa na Air Info Agadez ya ruwaito a ranar 11 ga Satumba.

    Sai dai har zuwa yanzu babu wata sanarwa a hukumance da ta tabbatar da sakin Eva Gretzmacher, ƴar Austria, da Claudia Abbt, ƴar Switzerland.

    An yi garkuwa da matan biyu ne daga gidajensu a Agadez a watan Janairu da Afrilu na 2025, yayin da wasu majiyoyi suka danganta sace su da ƙungiyar IS.

    Rahoton ya ce tun bayan da aka yi garkuwa da su, an yi ƙoƙarin ganin an sake su, amma ba a samu nasara ba.

    Wani ɗan uwan ɗaya daga cikin matan da aka yi garkuwa da su ya shaida wa Air Info Agadez cewa ba su da wani cikakken bayani da ke tabbatar da sakin ta, duk da cewa sun shafe kwanaki suna jiran samun labari mai daɗi.

    Abbt ta shafe shekaru da dama tana zaune a Agadez tare da mijinta ɗan Nijar. Babu wata ƙungiya da ta fito ta ɗauki alhakin sace ta.

    Gretzmacher, mai shekara 73, ta shafe shekara 28 tana zaune a Agadez kafin a yi garkuwa da ita. Ita ce ta kafa ƙungiyar Amanay, kuma ta kasance mai ruwa da tsaki a ayyukan da suka shafi ilimi da ƙarfafa mata da kare muhalli da al'adu da fasaha.

  2. MDD ta yi gargaɗi kan yaƙin basasar Yemen

    Wakili na musamman na Majalisar Ɗinkin Duniya kan Yemen ya yi gargaɗin cewa wajibi ne ƙasashen duniya su tunkari wani abin da ya kira sabon mataki mafi haɗari na yaƙin basasar ƙasar.

    Hans Grundberg ya ce kwace tashar jiragen ruwa ta Mokha ya bai wa ƙungiyar Houthi mai samun goyon bayan Iran damar kasancewa kai-tsaye a wata muhimmiyar hanya da jiragen ruwa ke bi a duniya.

    Tashar jirgin ruwan ta Mokha na kan Mashigar Bab al-Mandeb, wadda muhimmiyar mashigar ruwa ce da ke da matuƙar tasiri ga safarar mai daga Saudiyya da kuma kasuwancin duniya.

  3. Me ya faru a harin 11 ga Satumba, kuma mutum nawa ne suka mutu?

    Shekara 25 ke nan tun bayan harin da aka kai a ranar Talata, 11 ga Satumba, 2001, lokacin da wasu maharan ƙunar baƙin-wake suka yi juya akalar jiragen fasinja na Amurka, tare da yi musu dirar-mikiya a kan manyan gine-gine biyu a birnin New York, lamarin da ya yi sanadiyar mutuwar dubban mutane.

    A yau ne za a gudanar da bikin tunawa da waɗanda suka rasa rayukansu a harin a Amurka, inda ake sa ran gudanar da bukukuwa da wasu shirye-shirye daban-daban.

  4. Trump ya ƙi amincewa da buƙatar Saudiyya ta kai wa mayaƙan Houti hari

    A cewar Axios, Yariman Saudiyya mai jiran gado, Mohammed bin Salman, ya kira Shugaban Amurka Donald Trump sau biyu a ranar Alhamis, inda ya buƙaci shugaban na Amurka ya kai hari kan mayaƙan Houti.

    A lokaci guda, ƴan Houtin da Iran ke mara wa baya suna ci gaba da kutsawa tare da ƙwace iko da tashar jiragen ruwa ta Mocha, lamarin da ke ƙara musu iko a yankin mashigar ruwan Bab al-Mandab.

    Rahoton ya ce Mista Trump bai amince da wannan buƙata ba, yayin da jami'an Amurka suka jaddada cewa a halin yanzu gwamnatin Amurka ba ta da wani shiri na shiga yaƙi kai tsaye da mayaƙan Houti.

    A safiyar yau kuma, Ma'aikatar Harkokin Wajen Iran ta fitar da wata sanarwa inda ta yi kira da a kawo ƙarshen katange hanyoyin shiga Yemen ta soji, sannan a fara tattaunawa.

  5. Farawa

    Masu bibiyarmu a wannan shafi na kai tsaye daga BBC Hausa muna muku barka da safiyar ta Juma'atu babbar rana.

    Za ku iya ziyartar shafukanmu na sada zumunta domin kallon wasu hotuna da bidiyon hirarraki da muke wallafawa tare da yin tsokaci a kai.