KAI TSAYE, Abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya

Wannan shafi ne na kai tsaye da ke kawo muku labaran abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya a ranar Juma'a 11/09/2026

Tsallake Bidiyo ka ci gaba
  • Adeyemi Adeniyi
  • Abdourahamane Tchiani
  • Atiku Abubakar
  • NFF
  • Badriyyah Tijjani Kalarawi
  • Ranar Hausa: BBC
  • Danjuma Goje
  • Zainab
  • BBC
  • ABU
  • xxx
  • xxx
  • Khalifa Dokaji
  • Sheikh Jingir

Rahoto kai-tsaye

Isiyaku Muhammed

  1. MDD ta yi gargaɗi kan yaƙin basasar Yemen

    Yemen

    Asalin hoton, Getty Images

    Wakili na musamman na Majalisar Ɗinkin Duniya kan Yemen ya yi gargaɗin cewa wajibi ne ƙasashen duniya su tunkari wani abin da ya kira sabon mataki mafi haɗari na yaƙin basasar ƙasar.

    Hans Grundberg ya ce kwace tashar jiragen ruwa ta Mokha ya bai wa ƙungiyar Houthi mai samun goyon bayan Iran damar kasancewa kai-tsaye a wata muhimmiyar hanya da jiragen ruwa ke bi a duniya.

    Tashar jirgin ruwan ta Mokha na kan Mashigar Bab al-Mandeb, wadda muhimmiyar mashigar ruwa ce da ke da matuƙar tasiri ga safarar mai daga Saudiyya da kuma kasuwancin duniya.

  2. Me ya faru a harin 11 ga Satumba, kuma mutum nawa ne suka mutu?

    Satumba

    Asalin hoton, Getty Images

    Shekara 25 ke nan tun bayan harin da aka kai a ranar Talata, 11 ga Satumba, 2001, lokacin da wasu maharan ƙunar baƙin-wake suka yi juya akalar jiragen fasinja na Amurka, tare da yi musu dirar-mikiya a kan manyan gine-gine biyu a birnin New York, lamarin da ya yi sanadiyar mutuwar dubban mutane.

    A yau ne za a gudanar da bikin tunawa da waɗanda suka rasa rayukansu a harin a Amurka, inda ake sa ran gudanar da bukukuwa da wasu shirye-shirye daban-daban.

  3. Trump ya ƙi amincewa da buƙatar Saudiyya ta kai wa mayaƙan Houti hari

    Amurka

    Asalin hoton, Getty Images

    A cewar Axios, Yariman Saudiyya mai jiran gado, Mohammed bin Salman, ya kira Shugaban Amurka Donald Trump sau biyu a ranar Alhamis, inda ya buƙaci shugaban na Amurka ya kai hari kan mayaƙan Houti.

    A lokaci guda, ƴan Houtin da Iran ke mara wa baya suna ci gaba da kutsawa tare da ƙwace iko da tashar jiragen ruwa ta Mocha, lamarin da ke ƙara musu iko a yankin mashigar ruwan Bab al-Mandab.

    Rahoton ya ce Mista Trump bai amince da wannan buƙata ba, yayin da jami'an Amurka suka jaddada cewa a halin yanzu gwamnatin Amurka ba ta da wani shiri na shiga yaƙi kai tsaye da mayaƙan Houti.

    A safiyar yau kuma, Ma'aikatar Harkokin Wajen Iran ta fitar da wata sanarwa inda ta yi kira da a kawo ƙarshen katange hanyoyin shiga Yemen ta soji, sannan a fara tattaunawa.

  4. Farawa

    Masu bibiyarmu a wannan shafi na kai tsaye daga BBC Hausa muna muku barka da safiyar ta Juma'atu babbar rana.

    Za ku iya ziyartar shafukanmu na sada zumunta domin kallon wasu hotuna da bidiyon hirarraki da muke wallafawa tare da yin tsokaci a kai.