KAI TSAYE, Muhimman abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya 23/07/2026

Wannan shafi ne da ke kawo muku muhimman abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya na ranar Alhamis 23 ga watan Yuli, 2026.

Rahoto kai-tsaye

Haruna Kakangi, Isiyaku Muhammad

  1. Yadda aka yi wa manoma sama da 20 kisan gilla a Zamfara - Amnesty

    Gwamnan jihar Zamfara Dauda Lawal

    Asalin hoton, FB/Dauda Lawal

    Bayanan hoto, Gwamnan jihar Zamfara Dauda Lawal

    Sama da mutum 20 ne mahara suka kashe a jihar Zamfara da ke arewa maso yammacin Najeriya, yankin da ya daɗe yana fama da matsalar ƴan bindiga masu satar mutane domin neman kuɗin fansa.

    Lamarin wanda ya faru a ranar Laraba ya rutsa da manoma waɗanda suka raja'a wajen aikin gona.

    Wani wanda ya ga abin da ya faru ya shaida wa BBC cewa: "Muna gona muna aiki aka ce ga su nan sun taho, kafin mu ankara sun riga sun rufe mu, sun rufe ko ina, idan ka gudu sai su buge ka da mashin su harbe ka sannan su take ka.

    "Sun zo ne a babura sun kai 100, suka riƙa bin mutane suna kashewa, sannan suka tattara dabbobi suka tafi da su," in ji mazaunin ɗaya daga cikin ƙauyukan.

    Ya ƙara da cewa maharan sun fito ne daga "wajen Jangebe", wani yanki na jihar ta Zamfara da ya yi ƙaurin suna kan matsalar tsaro.

    "A halin yanzu muna cikin jeji ne, da idona na ga gawarwaki sun kai 20".

    Ya ce ƴan bindigar sun kai harin ne a ƙauyuka Sauna, Tudun Namale, Tsangaya, Mashekari da kuma Unguwar Shanu.

    A wani bayani da ta wallafa shafinta na facebook, ƙungiyar Amnesty International ta ce lamarin ya yi sanadin rayuka 24, yayin da mutane da dama suka tsira da munanan raunuka.

    "Wannan na nuni da cewa dabarar da ake amfani da ita wajen yaƙi da matsalar tsaro a jihar Zamfara ba ta aiki", in ji Amnesty.

    Ƙungiyar ta ce ƴan bindiga na kai hare-hare a ƙauyukan Zamfara a duk lokacin da suka ga dama, inda suke sanar da mazauna ƙauyuka a lokacin da za su kawo hari, sannan kuma sukan buƙaci a biya su maƙudan kuɗaɗe.

    Zamfara ta shafe sama da shekara 10 tana fama da matsalar ƴan fashin daji masu kai hare-hare suna kashe mutane da kuma garkuwa da wasu domin neman kudin fansa.

    Matsalar ta kuma shafi sauran jihohin yankin, kamar Katsina, Sokoto, Kebbi Kaduna da kuma Neja a arewa ta tsakiyar ƙasar.

    An yi amannar cewa akwai ƙungiyoyin yan bindiga da dama da suke cin karensu babu babbaka a dazukan da suka haɗa jihohin yankin har zuwa kudu maso yammacin ƙasar.

    A baya-bayan nan an samu lokutan da irin waɗannan mayaƙa ke kai hari a ƙauyuka suna kashe mutane tare da ƙona gidaje da kadarori.

    Hukumomi a ƙasar sun sha nanata cewa suna daukar matakai kan lamarin, amma har yanzu abin ya ci tura.

  2. Mun kai sabbin hare-hare kan sansanonin Amurka a Kuwait - Sojin Iran

    Sashen yaɗa labarai na rundunar juyin juya hali ta Iran ya ta fitar da wata sanarwa inda ta bayyana cewa ƙasar ta ƙaddamar da sabbin hare-hare kan sansanonin sojin Amurka uku a ƙasar Kuwait.

    Bayanin ya ce sansanonin su ne: Sansanin sojin Ali al-Salem da kuma na Arifjan, wadanda aka yi amfani da jirage marasa matuƙa wajen kai musu hari a yau.

    Sai kuma sansanin Doha, wanda ya ƙunshi rumbun ajiye makamai da kayan aiki na sojojin Amurka.

  3. An kwashe dare na 12 ana musayar wuta tsakanin Iran da Amurka

    xx

    Asalin hoton, Getty Images

    Bayanan hoto, Shugaban Amurka Donald Trump da jagoran Iran Mojtaba Khamenei

    Sojojin Amurka sun ce sun kai hare-hare a kan Iran na dare na 12 a jere. Kafofin yaɗa labarai na Iran sun ruwaito cewa an ji ƙarar fashewa a kusa da birnin Bushehr.

    Iran ma ta ci gaba da mayar da martani, inda ƙasar Kuwait ta ce garkuwarta ta sararin samaniya ta yi nasarar kakkaɓe wasu jirage marasa matuƙa da ta bayyana a matsayin na abokan gaba.

    Dakarun juyin-juya-hali na Iran sun yi ikirarin cewa wani jirgin dakon ɗanyen mai ya kama da wuta a wani yanki da aka dasa nakiyoyi a kusa da mashigar Hormuz, yayin da wasu jiragen dakon mai biyu suka juya baya.

    Jami’an tsaron Iran sun sake jaddada cewa ba za a bari wani jirgin dakon mai ya ratsa Mashigar ba, ba tare da haɗin kai ko amincewar Iran ba.

  4. Ƙungiyar Houthi mai goyon bayan Iran ta fara kai wa jiragen ruwa hari

    Yahya Saree, mai magana da yawun rundunar sojin ƙungiyar ƴan Houthi

    Asalin hoton, Getty Images

    Bayanan hoto, Yahya Saree, mai magana da yawun rundunar sojin ƙungiyar ƴan Houthi

    Ƙungiyar Houthi da ke Yemen, wadda Iran ke mara wa baya, ta ce ta kai hari kan jiragen ruwa na dakon mai na Saudiyya guda biyu a tekun Maliya.

    Dama akwai rahotanni da ke cewa wasu jiragen ruwa na dakon mai na sauya hanya, bayan da mayaƙan Houthi suka gargaɗi jiragen ruwa da su kauce wa tashoshin ruwa na Saudiyya.

    Kamfanin dillancin labarai na hukumar Saudiyya ya tabbatar da cewa harin da aka kai ya samu ɗaya daga cikin jiragen, mai suna Encelia, har gobara ta tashi a cikinsa.

    Saudiyya ta bayyana harin a matsayin saɓa wa dokokin ƙasa da ƙasa.

    A halin yanzu, akwai ƙarin fargaba cewa matakin da mayakan Houthin ke ɗauka na hana zirga-zirgar jiragen ruwa zai iya haddasa tashin gwauron zabi a farashin man fetur a duniya.

  5. Barka da warhaka!

    Barka da zuwa shafin BBC Hausa na kai-tsaye a wannan rana ta Alhamis - Tabawa ranar samu- inda muke kawo muku muhimman abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya.

    Za ku iya shiga zaurenmu na BBC Hausa WhatsApp domin samun labarai da ɗumi-ɗuminsu kuma ku yi shiyarin.

    Haka nan za ku iya tofa albarkacin bakinku a shafukanmu na facebook, instagram, X da kuma YouTube.