Amurka ta gargaɗi 'yan kasarta da ke zaune a Mali

Rundunar sojin Mali ta ce ƴanbindiga sun ƙaddamar hare-haren haɗin gwiwa a birane da dama da suka haɗa da Bamako baban birnin ƙasar.
Ƴan tawayen Azwad sun sanar da ƙwace muhimman yankuna a birnin Kidal bayan rahoton ɓarkewar rikici a Gao.
Wasu rahotanni da ba a tantance ba sun ce, wata ƙungiya mai alaka da al'Qaeda wadda a baya bayan nan ke neman haɗin kan yan tawayen Azawad na cikin rikicin.
Tuni ofishin jakadancin Amurka a Bamako ya gargadi Amurkawa mazauna Mali su nemi mafaka.


















