'ICPC ta hana El-Rufia damar samun kulawar aisibiti'

Asalin hoton, Muyiwa Adekeye/X
Mai ba tsohon gwamnan Jihar Kaduna, Nasir El-Rufai shawara kan harkokin yaɗa labarai, Muyiwa Adekeye, ya zargi hukumar ICPC da hana shi damar samun kulawar asibiti yayin da yake tsare.
A cikin wata sanarwa da ya fitar, Adekeye ya ce El-Rufai ya koka kan matsalar idanusa suna ƙaiƙayi da kumburi, inda ya nemi a kai shi asibiti domin duba lafiyarsa, amma jami’an ICPC suka ƙi amincewa da bukatar.
Ya bayyana cewa an riga an kai shi asibitin ido a ranar 4 ga watan Yuni, amma daga baya yanayin idon ya ƙara taɓarɓarewa, abin da ya jawo damuwa ga iyalansa.
A cewarsa, jami’an ICPC sun ga halin da idanuwansa ke ciki, amma ba a shirya masa ƙarin kulawar likita ba, abin da ya ce ya ƙara dagula lamarin.
Ya kuma zargi hukumar da bayar da bayanan da ba su dace ba ga iyalan El-Rufai, inda aka ce bai nemi ganin likita ba, zargin da ya ce ba gaskiya ba ne.
Adekeye ya kuma ce akwai umarnin kotu da ke ba El-Rufai damar samun kulawar lafiya, amma har yanzu ba a bi umarnin yadda ya kamata ba.
ICPC dai ba ta mayar da martani kai tsaye kan waɗannan zarge-zarge ba, yayin da batun ke ci gaba da jawo ce-ce-ku-ce.













