Peter Obi ya tabbatar da ficewa daga jam'iyyar ADC
Tsohon ɗan takarar shugaban Najeriya a zaɓen 2023, kuma jigo a jam'iyyar ADC ta masu haɗaka, Peter Obi ya tabbatar ficewa daga jam'iyyar.
Cikin wani saƙo da ya wallafa a shafinsa na X a ranar Lahadi, Peter Obi ya ce ya ɗauki matakin ne sakamakon rigingimun cikin gida da suka dabaibaye jam'iyyar.
Mista Obi ya ce rigimar da ya yi ƙoƙarin guje wa a tsohuwar jam'iyyarsa ta LP, ta sake kunno kai a cikin sabuwar jam'iyyar da ya shiga ta ADC.
Ya kuma bayyana cewa ya ɗauki matakin ne ba don wani shugaba ko jigo a cikin ADC ya ɓata masa rai ba.
''Ban ɗauki matakin saboda shugaban jam'iyyar, David Mark ko Atiku ko wani jigo a jam'iyyar ya yi min wani abu ba'', in ji shi.
Jam'iyyar ADC na fuskantar rikicin shugabanci, wanda yanzu haka ke gaban Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja, inda Nafi'u Bala ya shigar da ƙarar tsagin David Mark da cewa ba halastattun shugabanni ba ne.
A makon mai ƙarewa ne Koton Kolin ƙasar ta ce ɓangarorin biyu su koma babbar kotun tarayyar domin ci gaba da shari'ar.
Tun a cikin makon ne kuma ake ta raɗe-raɗin cewa Peter Obi da Kwankwaso za su fice daga jam'iyyar ADC zuwa NDC, kodayake kawo yanzu ba su tabbatar da hakan ba.
Shi ma kwankwason a wata sanarwa da ya fitar a ranar Asabar, ya ce yana tuntuɓar abokan siyasarsa domin ɗaukar mataki kan makomarsa a siyasance.