Harin Amurka ya kashe jami’an Rundunar Sararin Samaniya ta IRGC huɗu

Asalin hoton, Reuters
Ofishin Hulɗa da Jama'a na Rundunar Tsaron Juyin Juya Halin Musulunci ta Iran (IRGC) a lardin Kermanshah ya bayyana a cikin wata sanarwa cewa mambobi huɗu na Rundunar Sararin Samaniya ta IRGC a lardin sun mutu sakamakon harin da Amurka ta kai.
Ba a bayyana ƙarin cikakkun bayanai game da lamarin ba.
A daren jiya, bayan hare-haren Amurka, mataimakin gwamnan lardin Kermanshah ya ce babu wani yanki na lardin Kermanshah da aka kai wa hari.
A cewar kafafen yaɗa labarai na Iran, mataimakin kwamandan Rundunar Seyyed al-Shohada a birnin Diyar ya kuma ce a yau cewa mayaƙan Basij uku sun mutu, yayin da wasu da dama suka jikkata a harin da aka kai kan tsibirin Lavan.



















