KAI TSAYE, Abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya 31/08/2026

Wannan shafi ne da ke kawo muku abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya na ranar Litinin 31 ga watan Agustan 2026.

Tsallake Bidiyo ka ci gaba
  • Atiku Abubakar
  • NFF
  • Badriyyah Tijjani Kalarawi
  • Ranar Hausa: BBC
  • Danjuma Goje
  • Zainab
  • BBC
  • ABU
  • xxx
  • xxx
  • Khalifa Dokaji
  • Sheikh Jingir
  • Kano
  • Seriki Abbas
  • xxx

Rahoto kai-tsaye

Daga Aisha Babangida da Usman MINJIBIR

  1. Wani jirgin dakon mai ya kama da wuta bayan taka nakiyoyin ruwa a Hormuz - Iran

    ....

    Asalin hoton, Getty Images

    Rundunar juyin juya halin Iran (IRGC) ta ce wani babban jirgin dakon mai ya kama da wuta tare da tsaya wa cak bayan ya taka nakiyoyin ruwa biyu a kudancin mashigar Hormuz.

    A cewar rundunar, jirgin na ƙoƙarin bi ta wata hanya da ta bayyana a matsayin haramtacciya.

    A wata sanarwa da kafafen yaɗa labaran Iran suka wallafa, IRGC ta ce duk wani jirgin ruwa da ya karya dokokin tsaro da ta kafa a mashigar Hormuz zai iya fuskantar irin wannan sakamako.

    Har yanzu ba a bayyana sunan jirgin dakon man ba ko ƙasar da yake ɗauke da rajista.

    IRGC ta kuma jaddada cewa dukkan jiragen ruwa masu bi ta mashigar Hormuz wajibi ne su bi ƙa’idojin zirga-zirga da rundunar ruwanta ta gindaya.

    Ta kuma gargaɗi masu jiragen da kada su bari Amurka ta rinjaye su wajen amfani da wasu hanyoyi dabam, tana mai cewa hakan na iya jefa jiragen da ma’aikatansu cikin haɗari.

  2. Shugaban Iran ya isa Kyrgyzstan yayin da ake shirin ganawarsa da Putin

    ....

    Asalin hoton, Getty Images

    Shugaban Iran, Masoud Pezeshkian, ya isa birnin Bishkek na Kyrgyzstan domin halartar taron shugabannin ƙasashen ƙungiyar Haɗin Kan Ƙasashen Shanghai, yayin da ake sa ran zai gana da Shugaban Rasha Vladimir Putin a gefen taron.

    Pezeshkian ya isa Kyrgyzstan tare da Ministan Harkokin Wajen Iran, Abbas Araghchi, inda mataimakin firaministan ƙasar ya tarbe su a babban birnin Bishkek.

    Ana sa ran shugabannin ƙasashe 21 za su halarci taron, ciki har da na China, Rasha, Kazakhstan, Indiya da Iran.

    Kamfanin dillancin labaran IRNA ya ce ganawar da ake sa ran za ta gudana tsakanin Pezeshkian da Putin ita ce ta shida tsakanin shugabannin biyu.

  3. Iran ta ce ta kai hari kan sojojin Amurka a Jordan

    ....

    Asalin hoton, Getty Images

    Iran ta ce ta harba makamai masu linzami da jiragen yaƙi marasa matuƙa kan sansanonin sojin Amurka biyu da ke Jordan, bayan Amurka ta kai hari kan wasu wuraren harba makamai na Iran a tsibirin Larak.

    Iran ta ce harin na Amurka ya kashe tare da jikkata sojoji da fararen hula, kuma ta yi alƙawarin ramuwar gayya.

    Jordan ta ce ta kakkaɓo makamai masu linzami takwas da suka shiga sararin samaniyarta da sanyin safiyar Litinin.

    A halin da ake ciki, farashin ɗanyen mai ya ƙaru da sama da kashi 2%, inda farashin Brent ya haura dala 90 kan kowace ganga.

  4. Assalamu alaikum

    Jama'a barkanmu da wannan safiya ta Litinin daga wannan shafin namu na BBC Hausa, inda za mu ci gaba da kawo muku labaran kai-tsaye na abubuwan da suke faruwa a Najeriya da sassan duniya.

    Aisha Babangida ce za ta kasance da ku a daidai wannan lokaci.

    Za ku iya leƙawa shafukanmu na sada zumunta na facebook da X da kuma whatsapp domin karanta wasu labaran da kallon bidiyo da ma tafka muhawara.

    Ku kasance tare da mu.