Najeriya ta yi Allah-wadai da sabbin hare-haren Houthi a Saudiyya

Asalin hoton, Getty Images
Gwamnatin Najeriya ta yi Allah-wadai da sabbin hare-haren da mayaƙan Houthi a Yemen suka kai wa Saudiyya ranar Litinin 7 ga Satumba 2026, waɗanda suka jikkata fararen hula da dama tare da lalata wasu muhimman gine-ginen farar hula.
A wata sanarwa da kakakin ma'aikatar Oluwafemi Adeniyi ya fita, Najeriya ta ce tana kallon sabbin hare-haren a matsayin babbar barazana ga tsaro da ikon Saudiyya, da kuma zaman lafiyar yankin Gabas ta Tsakiya.
Gwamnatin Najeriya ta yi kira ga dukkan ɓangarorin da abin ya shafa da su mutunta dokokin ƙasa da ƙasa, kuma su yi taka-tsantsan tare da kauce wa duk wani mataki da ka iya ƙara ruruta rikicin.
Ta ce ƙara dagulewar lamarin na iya jefa rayukan fararen hula cikin haɗari, barazana ga tsaron yankin da kuma ƙara kawo cikas ga samar da makamashin da ake buƙata a duniya.
"Najeriya na goyon bayan gwamnati da al’ummar Saudiyya a wannan lokaci mai wahala, tare da yi wa waɗanda suka jikkata fatan samun sauƙi cikin gaggawa," in ji sanarwar.
Ma’aikatar Harkokin Wajen Najeriya ta kuma jaddada cewa gwamnati za ta ci gaba da goyon bayan matakan samar da zaman lafiya da sasanta rikice-rikice da za su taimaka wajen tabbatar da zaman lafiya a yankin.






















