Kana amfani da shafin BBC mai bayyana rubutu kawai (babu hoto) domin rage cin data. Idan ana so a ga hotuna da bidiyo sai a koma babban shafinmu.

Koma shafi mai hoto

Samu ƙarin bayani kan shafin tattalin data

KAI TSAYE, Yaƙin Iran da sauran abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sassan duniya Wannan 31/05/2026

Wannan shafi ne da kawo muku muhimman bayanan dangane da wainar da ake toyawa a Najeriya da sassan duniya na ranar Lahadi 31 ga watan Mayun 2026.

Taƙaitattu

Rahoto kai-tsaye

Daga Aisha Babangida

  1. Ba za mu amince da duk wata yarjejeniya ba sai mun tabbatar za a biya mu diyya - Iran

    Shugaban Majalisar Dokokin Iran, Mohammad Bagher Ghalibaf, ya bayyana cewa Iran ba za su amince da kowace yarjejeniya ba har sai sun tabbatar an kare haƙƙin al’ummar kasar gaba ɗaya.

    A jawabin da ya yi kafin fara zangon shekara ta uku na majalisar, Qalibaf ya ce sakon Jagoran Juyin Juya Halin Musulunci shi ne abun da za su yi amfani da shi yana mai jaddada cewa ba za a dogara da kalmomin makiya ba.

    Ya kuma ce dole ne majalisa ta guji rikice-rikicen da ke lalata aiki, tare da mayar da hankali kan batutuwan da suka shafi al’umma kai tsaye, musamman wajen tabbatar da sakamako mai kyau a fili ga jama’a.

    A bangaren dangantakar kasa da kasa, rahotanni daga kafafen yada labarai na Amurka sun ce shugaban Amurka, Donald Trump, ya kara tsaurara sharuɗɗa a sabon daftarin farko na yarjejeniya da Iran, inda aka ce an tura shi zuwa Tehran don nazari.

    A gefe guda kuma, sojojin Isra’ila sun ce suna ci gaba da faɗaɗa hare-haren a kudancin Lebanon, abin da ke ƙara tayar da hankali a yankin Gabas ta Tsakiya.

  2. Makinde ya kai ziyara ga iyalan ɗalibai da malaman da aka sace a Oyo

    Gwamnan Jihar Oyo, Seyi Makinde, ya tabbatar wa iyalan ɗalibai da malamai da aka sace a Karamar Hukumar Oriire cewa gwamnatinsa na yin duk mai yiwuwa domin ganin an ceto su lafiya.

    Makinde ya bayyana hakan ne a ranar Asabar yayin wata ziyara da ya kai garin Ahoro-Esiele, inda ya gana da iyalan waɗanda abin ya shafa da shugabannin al’umma da mazauna yankin a harabar makarantar L.A. Basic School.

    Ziyarar ta zo ne a daidai lokacin da al’umma ke cikin damuwa da fushi kan sace ɗalibai da malamai da dama, lamarin da ya kara tayar da hankalin jama’a kan tsaron makarantu a jihar.

    A cikin sakon da ya wallafa a shafinsa na X, gwamnan ya ce ya saurari korafe-korafen iyalan tare da sake tabbatar musu da cewa gwamnati na aiki ba dare ba rana domin ganin an dawo da waɗanda aka sace gidajensu lafiya.

    Sace ɗaliban ya faru ne a ranar 15 ga Mayu, lokacin da wasu ‘yan bindiga suka kai hari makarantu uku a yankin Esiele, inda suka tafi da dalibai da malamai 45.

    Bayan ‘yan kwanaki, rahotanni sun ce ɗaya daga cikin malaman da aka sace, wanda ake zargin malamin lissafi ne, an kashe shi.

    Lamarin ya jawo matukar allawadai daga jama’a, inda gwamnati da Shugaba Bola Ahmed Tinubu suka yi alkawarin ɗaukar mataki domin kubutar da waɗanda aka sace da kuma hukunta masu laifi.

  3. Faransa ta nemi taron gaggawa na MDD bayan Isra'ila ta karɓe gidan tarihi a Lebanon

    Ministan harkokin wajen Faransa, Jean-Noël Barrot, ya sanar da cewa Faransa ta nemi a kira taron gaggawa na Kwamitin Tsaro na Majalisar Dinkin Duniya bayan rahoton kwace tsohon katanga mai tarihi na Beaufort da sojojin Isra’ila suka yi a Lebanon.

    Barrot ya bayyana hakan ne a tashar talabijin na BFM, inda ya ce duk da cewa Faransa na amincewa da ‘yancin Isra’ila na kare kanta, babu wani dalili da zai halatta ci gaba da ayyukan soji da fadada shiga cikin yankin Lebanon.

    Ya nuna damuwa kan yadda ake kara faɗaɗa kasancewar sojojin Isra’ila a ƙasar Lebanon, yana mai cewa dole ne Majalisar Tsaro ta duba lamarin cikin gaggawa.

    A gefe guda, Ministan Tsaron Isra’ila ya sanar cewa an karɓe sansanin tarihi da muhimmanci na Shaqif (Beaufort), inda ya ce sojojinsa sun sake komawa wurin bayan shekaru 44 tun daga yakin Lebanon na 1982, sannan suka daga tutar Isra’ila a wurin.

    Wannan katafaren gini mai tarihi yana da mahimmanci a fannin soja saboda yana bai wa mai rike shi damar ganin yawancin kudancin Lebanon, lamarin da ke kara masa muhimmancin dabarun yaki.

  4. An sace tsohon baban jami'in sojin Najeriya da matarsa a Katsina

    An sace tsohon babban jami’in sojan Najeriya kuma tsohon Daraktan Yada Labaran Tsaro, Manjo janar Rabe Abubakar, tare da matarsa a jihar Katsina da ke arewa maso yammacin Najeriya.

    Rahotanni sun ce an yi garkuwa da su ne a ranar Asabar yayin da suke kan hanyar zuwa wani bikin aure, inda ‘yan bindiga suka tare motarsu a yankin Matazu.

    Mai magana da yawun sojojin Najeriya, Michael Onoja, ya tabbatar da faruwar lamarin ga BBC a ranar Lahadi, yana mai cewa ana ci gaba da kokarin ceto su tare da bin diddigin wadanda suka sace su.

    Wata majiya ta ce direban motar ya samu nasarar tserewa duk da raunin harbin bindiga da ya samu, yayin da ma’auratan aka tafi da su zuwa cikin dazukan da ke kusa da yankin.

    Lamarin ya sake bayyana matsalar tsaro da ke addabar sassan arewa maso yammacin Najeriya, inda ake yawan samun garkuwa da mutane, satar shanu da hare-hare kan kauyuka daga ‘yan bindiga.

    Jihar Katsina na daga cikin yankunan da suka fi fuskantar wannan matsala a shekarun baya-bayan nan, lamarin da ke ci gaba da janyo damuwa a fadin kasar.

    Wannan hari ya biyo bayan wani hari da aka kai a kauyen Kiliya da ke karamar hukumar Dutsinma, inda aka kashe aƙalla mutane 16 a ranar Juma’a, yayin bukukuwan Sallar Layya.

  5. Na cika kashi 90 cikin 100 na alƙawuran da na wa mutanen Kano - Gwamna Abba

    Gwamnan Jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, ya bayyana cewa gwamnatinsa ta cika kusan kashi 90 cikin 100 na alƙawuran da ta yi wa al’ummar jihar cikin shekaru uku a kan mulki.

    Ya yi wannan bayani ne yayin da ya karbi bakuncin Sarkin Rano, Ambasada Muhammad Isa Umaru, wanda ya kai masa ziyarar Sallah a Fadar Gwamnatin Kano a ranar Asabar.

    A cikin wata sanarwa da kakakin gwamnan, Sanusi Bature Dawakin Tofa, ya fitar, ya ce gwamnatin Yusuf ta mayar da hankali kan aiwatar da ayyukan raya kasa da manufofi da suka shafi rayuwar al’umma kai tsaye a fannoni daban-daban.

    Ya bayyana cewa an samu ci gaba a fannonin ilimi, lafiya, ababen more rayuwa, noma, samar da ruwa, tallafawa matasa da bunkasa tattalin arziki, tare da cewa duk wadannan na nufin inganta rayuwar jama’a da kuma ciyar da Kano gaba mai dorewa.

    A nasa bangaren, Sarkin Rano ya yaba wa gwamnan bisa abin da ya kira manyan nasarori cikin shekaru uku, inda ya ambaci kammala hanyoyi mai tsawon kilomita biyar a Rano, Kibiya da Bunkure, da kuma ci gaban aikin ruwa na Kaluwaiwai.

  6. Jam’iyyar NDC ta tabbatar da Peter Obi da Kwankwaso a matsayin 'yan takararta

    Jam’iyyar Nigeria Democratic Congress (NDC) ƙarƙashin jagorancin Sanata Seriake Dickson ta bayyana tsohon gwamnan Jihar Anambra, Peter Obi, a matsayin dan takararta na shugaban kasa a zaben shekarar 2027.

    An bayyana Obi a matsayin wanda zai yi wa jam’iyyar takara ne a babban taron jam’iyyar da aka gudanar a Abuja ranar Asabar.

    Bayan karbar tutar jam’iyyar, Obi ya sanar da tsohon gwamnan Jihar Kano, Musa Kwankwaso, a matsayin abokin takararsa.

    Fitowar Obi a matsayin dan takarar NDC ya sake bude gasar neman shugabancin kasa tsakanin manyan 'yan siyasa uku.

    Wannan na zuwa ne bayan da Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya lashe tikitin takarar shugaban kasa na jam’iyyar APC, yayin da tsohon mataimakin shugaban kasa Atiku Abubakar ya zama dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar ADC.

    Atiku da Obi dai da farko sun shiga ADC tare da wasu manyan 'yan adawa a watan Yulin 2025 a wani yunƙuri na hada kan adawa domin ƙalubalantar APC a zaben 2027. Sai daga baya Obi ya fice daga ADC tare da Kwankwaso, inda suka koma NDC.

    Shigowar Obi da Kwankwaso cikin NDC tare da magoya bayansu na kungiyoyin Obidient Movement da Kwankwasiyya Movement ya ƙara wa jam’iyyar ƙarfi a fagen siyasa.

  7. Za a kammala batun gyaran gidajen da yaƙi ya lalata nan da Yuli - Iran

    Mai magana da yawun Gwamnatin Birnin Tehran, Abdul Motahar Mohammadkhani, ya bayyana cewa ana sa ran a kammala dukkan batutuwan da suka shafi sake gina da gyaran gidajen da yaƙin baya-bayan nan ya lalata nan da watan Yuli.

    Ya ce an samu kusan kashi 40 cikin 100 na ci gaba wajen sake gina gidajen da lalacewarsu ta kai ga buƙatar rushe su gaba daya tare da sake ginawa.

    Mohammadkhani ya kuma bayyana cewa gidaje kusan 51,000 ne suka samu matsala sakamakon yaƙin.

    Ya ƙara da cewa aikin gyaran gidajen da suka samu ƙananan lalacewa ya kai kashi 97 cikin 100, kuma ana sa ran za a kammala batutuwan da suka shafe su kafin ƙarshen wannan makon.

    A cewarsa, an dora babban nauyin gudanar da aikin sake gina gidajen da suka lalace a kan Gwamnatin Birnin Tehran.

    Mai magana da yawun ya kuma ce har yanzu ba a sanya takamaiman wa'adin lokacin da iyalan da ke zaune a otal-otal na wucin gadi za su bar wuraren ba.

    Ya bayyana cewa a lokacin da yaƙin ya fi tsanani, iyalai sama da 2,300 ne suka kasance a matsugunan gaggawa, amma yanzu adadin ya ragu zuwa iyalai 1,629.

  8. Iran ta ce ta kakaɓo jirgin yaƙin Amurka ƙirar MQ-1

    Rundunar juyin juya halin Musulunci ta Iran (IRGC) ta sanar da cewa ta harbo wani jirgin yaɓi maras matuki na Amurka ƙirar MQ-1 da ta kai mata hari da shi a safiyar yau

    A cikin wata sanarwa da sashen hulda da jama'a na rundunar ya fitar, ta ce jirgin ya yi yunkurin shiga sararin ruwan Iran domin gudanar da ayyukan da ta bayyana a matsayin na tada hankali, amma an gano shi cikin gaggawa tare da harbo shi ta amfani da makamai masu linzami na zamani na rundunar.

    Rahotannin kafafen yaɗa labaran Iran sun ce rundunar kariyar sararin samaniyar IRGC ta jaddada cewa yankunan ruwan ƙasar na ƙarƙashin cikakken kulawarta, kuma za ta mayar da martani cikin tsanaki ga duk wani yunƙurin keta huruminta.

    Ya zuwa yanzu, rundunar sojojin Amurka (CENTCOM) ba ta fitar da wata sanarwa ko martani kan wannan iƙirari da Iran ta yi ba.

  9. Assalamu alaikum

    Jama'a barkanmu da wannan safiya ta Lahadidaga wannan shafin namu na BBC Hausa, inda za mu ci gaba da kawo muku labaran kai-tsaye na abubuwan da suke faruwa a Najeriya da sassan duniya.

    Aisha Babangidda ke fatab sake kasancewa da ku a daidai wannan lokaci.

    Za ku iya leƙawa shafukanmu na sada zumunta na facebook da X da kuma whatsapp domin karanta wasu labaran da kallon bidiyo da ma tafka muhawara.

    Ku kasance tare da mu.