Watakila Palace ta ɗauki Sage a matakin sabon koci, Premier League
Ana sa ran kocin Lens, Pierre Sage, zai tattaunawa da Crystal Palace a farkon wannan mako yayin da ƙungiyar Premier League ke neman wanda zai maye gurbin Oliver Glasner.
Palace (wanda ake yi wa lakabi da Eagles) na fuskantar kalubale a kokarin ɗaukar Andoni Iraola, wanda ake sa ran zai fara tattaunawa a hukuma da Liverpool a kwanaki masu zuwa domin maye gurbin Arne Slot da aka kore a ranar Asabar.
Palace wadda ta lashe Conference League ta gabatar da tayin aiki mai tsoka ga Iraola, amma da alama yana kan hanyar zuwa wani wuri, yanzu Crystal Palace na duba wasu zaɓuɓɓuka daban.
Ƙungiyar ta kudancin London, ƙarƙashin jagorancin shugaba, Steve Parish, ba zai yi gaggawa wajen yanke hukunci ba kan sabon koci, domin suna nazarin wasu sunaye daban.
Daga cikin waɗanda ake dubawa akwai Sage, wanda ya yi suna a matsayin ɗaya daga cikin masu horarwa masu hazaka a Turai.
BBC Sport ce ta fara bayyana sha’awar Crystal Palace ga mai shekara 47 a ranar 8 ga Mayu, amma a lokacin shugabancin Palace ya fi mayar da hankali kan ƙoƙarin ɗauko Iraola daga Bournemouth.
Rahotanni sun ce kocin Lens ɗin da yiwuwar komawa Palace, kuma ana sa ran zai gana da jami’an ƙungiyar a cikin kwanaki masu zuwa.

Asalin hoton, Getty Images



