KAI TSAYE, Abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya, 07/09/2026

Wannan shafi ne da ke kawo muku labaran abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya, 07/09/2026

Rahoto kai-tsaye

Abdullahi Bello Diginza

  1. Mutum biyar sun mutu bayan jirgi ya yi hatsari a Amurka

    Jirgin dakon kaya

    Asalin hoton, Reuters

    Wani jirgin dakon kaya na kamfanin Amazon Air ya kauce daga titin saukar jiragen sama yayin da yake ƙoƙarin sauka a filin jiragen sama na Miami International Airport, lamarin da ya yi sanadin mutuwar mutum biyar tare da jikkata wasu biyar da munanan raunuka.

    Jirgin dakon kayan ƙirar Boeing 767-300 ya yi hatsarin ne jim kaɗan kafin ƙarfe biyu na rana agogon ƙasar (19:00 agogon GMT), bayan da ya tashi daga filin jirgin sama na Luis Muñoz Marín da ke San Juan, Puerto Rico.

    Har ila yau, jirgin ya bugi wasu motoci da ke kusa da wurin da hatsarin ya auku.

    Kamfanin Amazon ya ce yana "aiki kafaɗa da kafaɗa da hukumomi da sauran jami'an da abin ya shafa domin gano ainihin abin da ya faru."

    Hukumar Kula da Sufurin Jiragen Sama ta Amurka (FAA) ta dakatar da duk wani tashin da saukar jirage a filin jirgin saman, yayin da jami'an kashe gobara da na agajin gaggawa suka garzaya wurin da hatsarin ya faru.

    Hatsarin ya afku ne a daidai lokacin hutun Ranar Ma'aikata - ɗaya daga cikin lokutan tafiye-tafiye mafi yawan cunkoso a shekara.

    Magajin garin gundumar Miami-Dade, Daniella Levine Cava, ta bayyana a wani taron manema labarai da yammacin ranar Lahadi cewa, "Aƙalla mutum biyar ne suka rasa rayukansu, yayin da wasu biyar suka jikkata."

  2. Yaƙinmu da Rasha zai iya ci gaba har zuwa lokacin hunturu - Zelensky

    Volodymyr Zelensky ya ce yana sa ran ci za a ci gaba da gwabza yaƙi da Rasha har cikin lokacin hunturu.

    Ya bayyana haka bayan tattaunawarsa ta farko da jakadun Donald Trump a Kyiv-Jared Kushner da Steve witkoff.

    ''A yanzu mutane da dama a nan na shiryawa don tsananin da wannan rikici zai yi da kuma tsananin faɗa a lokacin hunturu,'' in ji shi.

    Amurkawan sun fara tattaunawa ta biyu da Shugaban Ukraine bayan sun yiwa ƙasashen ƙawance ƙarin haske.

    Mista Zelensky ya jaddada buƙatar ƙulla yarjejeniyar sulhun da ba za ta bai wa Rasha damar sake kai wani hari ba.

  3. Iran ta ce za ta sanar da sabon yankin tsaro a mashigar Hormuz

    Mohsen Rezaei

    Asalin hoton, Getty Images

    Babban jami'in tsaron Iran, Mohsen Rezaei, ya ce Iran za ta sanar da sabon yankin da aka sanya wa tsaro a wajen mashigin Hormuz.

    Ya ce yankin zai kai har zuwa wasu sassan Tekun Fasha.

    Duk jirgin ruwan da ya shiga yankin da nufin ketare mashigin ruwan, za a saka shi cikin jerin wadanda aka sanyawa takunkumi.

    Tun da farko, mai shiga tsakani na Iran Mohammad Ghalibaf, ya yi gargadin cewa Iran za ta dauki matakin mayar da martani mai tsanani cikin kan Amurka cikin gaggawa.

  4. Sallama

    Assalamu alaikum, masu bin shafin BBC Hausa kai-tsaye barkanmu d asafiyar wannan rana da Litinin, Mande tushen aiki ko da nasara na tsoronka, kamar yadda Hausawa ke yi wa kirari.

    Abdullahi Bello Diginza ke fatan kasancewa da ku a daidai wannan lokaci domin kawo muku halin da duniya ke ciki.

    Ku biyo mu a shafukanmu na sada zumunta domin tafka muhawara kan labaran da muke wallafawa.