Rundunar ƴansandan Najeriya ta kori jami'inta da ya kashe matashi a Delta

Asalin hoton, NIGERIA POLICE
Rundunar ƴansandan Najeriya ta ce ta kori wani jami'inta da ke dannu a kisan wani matashi Mene Ogidi a yankin Effurun da ke jihar Delta a Kudu Maso Kudancin ƙasar.
Rundunar ƴansandan a wata sanarwa da ta fitar a ranar Laraba, ta ce an sallami jami'in mai suna ASP Nuhu Usman bayan kammala bincikenta kamar yadda babban sufetan hukumar Tunji Disu ya ba da umarni.
A wata sanarwa a ranar Laraba mai dauke da sa hannun jami’in hulda da jama’a na rundunar, DCP Anthony Placid, ta ce an kama Ogidi mai shekaru 28 ne a lokacin da yake yunkurin aika wani saƙo da ake zargin bindiga ce da harsashi hudu, lamarin da ya yi sanadin mutuwar shi.
Hukumar ta ce bayan samun waɗannan rahotannin ne, aka dauƙi matakin mayar da binciken zuwa hedikwatarta da ke Abuja babban birnin ƙasar.
"Bincike ya nuna cewa cewa, jami'i ASP Nuhu Usman ya aikata laifin da ya ci karo da dokokin hukumar na 237 da kuma amfani da makami ba bisa ƙa'ida ba," in ji sanarwar.
"Abin da ya aikata, rashin ƙwarewa ne da kuma cin amanar rantsuwar da ya yi na kare rayuwar al'umma da dokokin ƙasa".
Rundunar ta ƙara da cewa bayan kammala matakan da suka dace, za a miƙa jami’an da abin ya shafa ga hukumomin shari’a da suka dace domin gurfanar da su.




