Kana amfani da shafin BBC mai bayyana rubutu kawai (babu hoto) domin rage cin data. Idan ana so a ga hotuna da bidiyo sai a koma babban shafinmu.

Koma shafi mai hoto

Samu ƙarin bayani kan shafin tattalin data

Abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya 27/07/2026

Wannan shafi ne da ke kawo muku abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya na ranar Litinin 27 ga watan Yunin 2026.

Taƙaitattu

Rahoto kai-tsaye

Daga Aisha Babangida, Haruna Kakangi da Muslim Muhammad Yusuf

  1. Za mu biya diyya daga kuɗaɗen Iran dake hannunmu - Trump

    Shugaban Amurka Donald Trump ya sake bayyana cewa gwamnatinsa za ta yi amfani da kuɗaɗen Iran da suke ƙarƙashin ikon Amurka wajen biyan diyya da kuma gyaran ɓarnar da ya ce ta faru sakamakon yaƙin baya-bayan nan.

    Trump ya bayyana hakan ne yayin da yake ganawa da ƴan jarida a cikin jirginsa, inda ya ce za a yi amfani da kuɗaɗen na Iran wajen biyan wasu daga cikin asarar da aka samu.

    Haka kuma shugaban Amurkan ya yi watsi da damuwar da ake nunawa cewa Amurka na iya fuskantar ƙarancin makamai bayan shafe kusan watanni biyar tana kai hare-hare kan Iran.

    Ya ce Amurka tana da tarin makamai da za su iya ci gaba da gudanar da duk wani aiki na soji idan buƙatar hakan ta taso.

    Trump ya ce, "Muna da makamai masu yawa iri-iri," inda ya ƙara da cewa ƙasar tana da isassun makamai fiye da abin da za ta iya amfani da shi a kowane yanayi.

  2. Gwamnatin Katsina ta ce dakarun tsaronta sun kashe ƴan bindiga 40 a Bakori

    Gwamnatin jihar Katsina ta ce dakarun rundunar tsaronta ta Community Watch Corps tare da haɗin gwiwar mafarauta sun daƙile wani harin ƴan bindiga a ƙauyen Guga da ke ƙaramar hukumar Bakori, inda suka kashe fiye da ƴan bindiga 40 tare da hallaka wasu manyan kwamandojinsu.

    Kwamishinan tsaro na jihar, Nasir Mu'azu, ne ya bayyana hakan a cikin wata sanarwa da ya fitar ranar Litinin.

    Ya ce harin ya faru ne da misalin ƙarfe 5:40 na yammacin ranar Lahadi, lokacin da sama da ƴan bindiga 200 masu ɗauke da muggan makamai suka mamaye ƙauyen Guga.

    "Jagoran harin shi ne fitaccen shugaban ƴan bindiga, Idi Abasu Aiki, tare da goyon bayan mambobin ƙungiyar Ado Aleru daga maƙwabciyar jihar Zamfara," in ji sanarwar.

    Gwamnatin ta ce bayanan sirri da ta samu tun kafin harin sun nuna cewa ƴan bindigar sun shirya korar mafarauta da jami'anta da ke kare al'ummomin yankin, kafin daga bisani su kai hare-hare kan garin Bakori da wasu ƙauyukan da ke makwabtaka da shi.

    Sai dai ta ce hakan ya ba su damar shirya martani cikin gaggawa, kuma an artabu sosai da ƴan bindigar

    Gwamnatin ta ce "fiye da ƴan bindiga 40 ne aka kashe, yayin da bayanan sirri da aka tattara daga baya suka nuna cewa kimanin manyan kwamandoji takwas na ƙungiyar su ma sun mutu a fafatawar."

    Ta kuma bayyana cewa ana kyautata zaton shugaban ƴan bindigar, Idi Abasu Aiki, ya samu munanan raunukan harbin bindiga.

  3. Zan ɗauki tsattsauran matakin soji kan Iran idan aka gaza cimma matsaya - Trump

    Shugaban Amurka Donald Trump ya ce ƙasarsa na gudanar da "tattaunawa mai zurfi sosai" da Iran, amma zai bayar da umarnin ɗaukar "matakin soji mai tsauri" idan aka gaza cimma matsaya.

    A wata hira da ya yi da kafar Axios, Trump ya ce ya bayar da umarnin dakatar da hare-haren da Amurka ke kaiwa Iran ne bisa buƙatar ƙasashen da ke shiga tsakani, domin a ba da damar ci gaba da tattaunawar.

    "Muna cikin tattaunawa mai da Iran. Idan ba ta yi nasara ba, za mu koma ci gaba da ayyukan soji masu tsanani," in ji Trump.

    Da aka tambaye shi tsawon lokacin da yake ganin zai a iya ci gaba da tattaunawa diflomasiyya, Trump ya ce lokacin ba zai yi tsawo ba.

    Shugaban na Amurka ya kuma yi magana kan ziyarar da Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu zai kai Washington, inda ya ce zai tattauna da shi kan batun yaƙin da Iran.

    Sai dai mai magana da yawun ma'aikatar harkokin wajen Iran ya ce babu wata tattaunawa da ake yi a halin yanzu tsakanin Tehran da Washington.

    Ya ce Iran ba za ta bari Amurka ta ƙayyade lokacin yaƙi ko zaman lafiya ba.

  4. Gwamnatin jihar Kebbi ta yi wa mutum 300 auren gata

    Gwamnan jihar Kebbi, Dakta Nasir Idris, ya ɗaura auren ma'aurata 300 a ƙarƙashin shirin auren gata da gwamnatin jihar ke gudanarwa.

    Shirin, wanda shi ne karo na uku a jihar, ya haɗa ma'aurata Musulmi da Kirista daga ƙananan hukumomi 21 na jihar.

    Gwamnan ne ya ɗaura auren, wanda mai ɗakinsa, Hajiya Nafisa Nasir Idris ta shirya domin taimaka wa mutanen da ke fuskantar ƙalubalen kuɗin aure.

    A cikin ma'auratan da aka yi wa auren, akwai mata 150 da mazajensu 150, inda gwamnatin jihar ta biya sadakin naira 250,000 ga kowace amarya da angonta.

    Baya ga biyan sadaki, gwamnatin jihar ta kuma samar wa ma'auratan kayan tallafi da suka haɗa da gadaje, kujeru, abinci da sauran abubuwan buƙata domin fara rayuwar aurensu.

    Gwamnatin Kebbi ta ce ta ware naira miliyan 75 domin gudanar da wannan shirin na auren gata, wanda ta ce yana daga cikin shirye-shiryen rage wa matasa nauyin kuɗin aure da ƙarfafa zaman iyali a jihar.

  5. Ƴan bindiga sun kashe sama da mutum 30 a jihar Kaduna

    Ƴan bindiga sun kashe sama da mutum 30 a wani ƙauye na ƙaramar hukumar Kauru da ke jihar Kaduna a arewa maso yammacin Najeriya.

    Kwamishinan yaɗa labarai na jihar Ahmed Maiyaki ya tabbatar wa BBC cewa an sace mutanen ne a wani hari da aka kai da sanyin safiyar Litinin.

    Ya ce ƴan bindigar sun kashe mutanen ne a ƙauyen Narido, inda kuma rahotanni suka ce da dama sun jikkata.

    A cewar ƙungiyar ci gaban kudancin Kaduna, SOKAPU, mutanen da aka kashe har da mata da ƙananan yara, inda aka raunata wasu da dama a harin.

    A wasiƙar da shugaban SOKAPU Engr Samuel Taraba ya fitar, ya nuna damuwa kan ƙaruwar hare-hare a yankin, musamman ƙananan hukumomin Kajuru, Chikun, Kauru da Zangon Kataf.

    Sai dai Maiyaki ya ce gwamnati jihar na ɗaukar matakan tsaro a yankin.

  6. Hukumomin Tigray sun amince da kasafin kuɗin da ya haura dala miliyan 400

    Hukumomin yankin Tigray da ke arewacin Habasha sun amince da kasafin kuɗin da ya haura dala miliyan 400, a daidai lokacin da rikici ke ƙara tsananta tsakaninsu da gwamnatin tarayyar ƙasar.

    Shugabannin yankin sun zargi gwamnatin Habasha da katse musu tallafin kuɗi da kuma hana al'ummar yankin samun muhimman ayyukan more rayuwa, abin da suka ce ya saɓa wa yarjejeniyar zaman lafiya da aka cimma wadda ta kawo ƙarshen yaƙin basasar ƙasar a shekarar 2022.

    Sun ce matakan da gwamnatin ke ɗauka na ci gaba da jefa yankin cikin mawuyacin hali tare da barazana ga zaman lafiyar da aka samu bayan yaƙin.

    Shugaban yankin Tigray, Debretsion Gebremichael, ya yi gargadin cewa idan aka ci gaba da wannan hali ba tare da warware matsalolin ta hanyar lumana ba, yankin zai ɗauki matakan kare kansa.

    Sai dai gwamnatin Habasha ba ta ce komai ba kan waɗannan zarge-zargen a halin yanzu.

  7. Sojojin Sudan sun ƙwace babbar hanyar Khartoum zuwa El-Obeid daga hannun RSF

    Sojojin Sudan sun sanar da cewa sun sake ƙwace ikon babbar hanyar da ta haɗa birnin Khartoum da arewacin El-Obeid a jihar Kordofan, bayan kwana biyu ana gwabza kazamin faɗa da mayaƙan rundunar RSF.

    Tun bayan ɓarkewar yaƙin basasar Sudan a watan Afrilun 2023, mayaƙan RSF ne ke iko da wannan babbar hanya mai tsawon kusan kilomita 350.

    Mai magana da yawun sojojin Sudan ya ce dakarunsu sun kuma ƙwace iko da garuruwa da ƙauyuka da dama a yankin, yayin da mayaƙan RSF suka tsere daga wuraren.

    Nasarar na zuwa ne yayin da Majalisar Ɗinkin Duniya ke ci gaba da gargadin tabarbarewar halin jin ƙai a birnin El-Obeid, inda ta ce kusan fararen hula 500,000 ke cikin mawuyacin hali sakamakon hare-haren bama-bamai da jirage marasa matuƙa da RSF ke kai wa.

    A wani rahoto kuma, Hukumar Lafiya ta Duniya (WHO) ta kiyasta cewa sama da mutum 400,000 ne suka mutu tun bayan fara yaƙin Sudan, yayin da fiye da mutane miliyan 15 suka rasa muhallansu sakamakon rikicin.

  8. Masu zanga-zangar da suka tilasta ministan ilimin India murabus sun nemi a saki waɗanda aka kama

    Matasan da suka jagoranci zanga-zangar da ta kai ga murabus ɗin ministan ilimi a Indiya sun buƙaci gwamnati ta saki dukkan mutanen da aka kama yayin zanga-zangar da aka shafe makonni ana yi a sassan ƙasar.

    Gangamin, wanda aka yi wa laƙabi da Cockroach Janta Party, ya fara zanga-zangar ne saboda zargin kwarmata takardun jarabawa kafin ɗalibai su rubuta su.

    Wakilin BBC ya ce jagororin gangamin sun yi zargin cewa baya ga kama masu zanga-zangar, jami'an tsaro sun kuma ci zarafin daruruwan mutane a babban birnin ƙasar da kuma wasu yankuna.

    Rahotanni sun ce har yanzu ana tsare da wasu daga cikin waɗanda aka kama a jihohin Assam, West Bengal da Bihar.

    A nata ɓangaren, gwamnatin Indiya ta sanar da amincewa da wasu daga cikin buƙatun masu zanga-zangar, ciki har da sakin dukkan mutanen da aka tsare a lokacin zanga-zangar.

  9. 'Yan kwana-kwana sun ce har yanzu ba a shawo kan gobarar daji a Faransa ba

    'Yan kwana-kwana sun ce har yanzu ba a shawo kan gobarar daji a Faransa ba

    Hukumomin kashe gobara a Faransa sun ce har yanzu suna fafutukar shawo kan gobarar daji da ke ci gaba da yaɗuwa a kudu maso gabashin ƙasar.

    Magajin garin birnin Bordeaux, Thomas Gaznav, ya ce hukumomi sun shirya tsaf domin fuskantar duk wani ƙalubale da ka iya tasowa sakamakon gobarar.

    Gobarar ta yi barna a yankunan Gironde da Var da Hautes-Côtes da kuma Landes, lamarin da ya tilasta kwashe kusan mutum 250,000 daga gidajensu.

    Sai dai gobarar ta ɗan lafa a wasu sassan kudu maso gabashin Faransa bayan da iska ta ragu tare da saukar ruwan sama da tsakar dare.

    Wani jami'in kashe gobara ya shaida wa BBC cewa sun samu nasarar shawo kan gobarar a wasu wurare, amma har yanzu ana ci gaba da aiki domin hana ta sake bazuwa.

    A nasa bangaren, Ministan Harkokin Cikin Gida na Faransa, Laurent Nunez, ya shaida wa taron kwamitin gwamnati kan lamarin cewa har yanzu ba a fita daga haɗari ba.

    "Har yanzu ba mu fita daga haɗari ba, saboda haka dole ne jama'a su ci gaba da bin matakan kariya," in ji Laurent Nunez.

  10. Sojojin Najeriya sun ceto wasu mutum biyu da aka sace a jihar Taraba

    Rundunar sojin Najeriya ta ce dakarunta ƙarkashin Operation Whirl Stroke sun ceto wasu mutum biyu da aka yi garkuwa da su a wani samame da suka kai a yankin Lande Jessi da ke karamar hukumar Lau a jihar Taraba.

    Sojojin sun bayyana cewa sun ƙaddamar da samamen ne bayan samun sahihan bayanan sirri cewa wasu masu garkuwa da mutane sun kai hari ƙauyukan Tashan Musa da Barkindan Fulani, inda suka sace mutane biyu tare da kwashe kayan abinci.

    Sanarwar da rundunar ta fitar ta ce lamarin ya faru ne a ranar 26 ga Yulin 2026.

    Bayan gudanar da bincike da sintiri a wurare daban-daban, dakarun sun samu nasarar ceto mutanen biyu da aka sace waɗanda aka ce sun shafe kusan mako guda a hannun masu garkuwa da mutanen kafin a kuɓutar da su.

    Rundunar ta ce nasarar aikin na nuna ƙudurinta na kare rayuka da dukiyoyin jama'a tare da ci gaba da yaƙi da dukkan nau'ikan laifuffuka a faɗin kasar.

  11. Shugaban Ukraine ya isa Birtaniya domin ganawa da firaminista Andy Burnham

    Shugaban ƙasar Ukraine, Volodymyr Zelensky, ya isa Birtaniya inda ake sa ran zai gana da firaministan ƙasar, Andy Burnham, cikin sa'a guda.

    Wannan ita ce ganawar farko da Burnham zai yi da wani shugaban ƙasa tun bayan da aka zaɓe shi a matsayin firaminista.

    Ya jaddada cewa Birtaniya za ta ci gaba da bayar da goyon baya ga Ukraine a yaƙin da take yi.

    Za a gudanar da ganawar ne a wani sansanin sojojin ruwa, sannan Zelensky zai kuma kai ziyara ga dakarun Ukraine da ke samun horo a Birtaniya.

    Ganawar na zuwa ne a wani lokaci da dangantakar tsaro da siyasa tsakanin Iran da ƙasashen biyu ke ci gaba da jan hankali a fagen siyasar duniya.

  12. Iran ta gayyaci jakadan Faransa kan zargin tsoma baki a harkokin cikin gidanta

    Ma'aikatar Harkokin Wajen Iran ta sanar da cewa ta gayyaci jakadan Faransa da ke Tehran domin nuna rashin jin dadinta kan abin da ta bayyana a matsayin tsoma bakin Faransa a harkokin cikin gidan kasar.

    Kakakin ma'aikatar, Ismail Baghaei, ya ce Faransa ta yi katsalandan a al'amuran cikin gida na Iran “ta hanyar amfani da ofishin jakadancinta da kuma hujjar hulɗa da ƙungiyoyin farar hula,” yana mai cewa ya kamata Faransa ta nemi afuwa kan hakan.

    Wannan mataki na Iran ya zo ne bayan ministan harkokin wajen Faransa, Jean-Noël Barrot, ya zargi jami'an tsaron Iran da karya kariyar diflomasiyyar wasu ma’aikatan ofishin jakadancin Faransa guda biyu a Tehran.

    A wani saƙo da ya wallafa a shafin X, Barrot ya ce an kama mutanen biyu tare da yi musu tambayoyi na tsawon sa’o’i ba tare da wani dalili ba.

    Bayan faruwar lamarin, Ma'aikatar Harkokin Wajen Faransa ta gayyaci jami’in diflomasiyyar Iran mai kula da harkokin ofishin jakadancin kasar a Paris domin bayyana damuwarta.

    Lamarin na ƙara dagula dangantaka tsakanin Iran da Faransa, yayin da ƙasashen biyu ke musayar zarge-zarge kan yadda ake mu’amala da jami’an diflomasiyya.

  13. Wane ne sojan Najeriya da ake zargi da sayar wa ƴanbindiga makamai?

    Rundunar sojin Najeriya ta ce dakarunta na Operation HADIN KAI sun kama wani soja da rundunar ta ayyana a matsayin wanda ake nema ruwa a jallo, bisa zarginsa da sayar wa da ƴanbinga da sauran masu aikata laifuka makamai ba bisa ƙa’ida ba.

    Sanarwar da rundunar ta fitar ta ce an kama Mohammed Yusuf ne da misalin karfe 6:30 na yammacin ranar 25 ga watan Yulin 2026 a tashar motoci ta Jidari da ke Maiduguri bayan samun sahihan bayanan sirri.

    Binciken farko ya nuna cewa Mohammed Yusuf ya tsere daga sansaninsa tun ranar 7 ga watan Yulin 2026 kafin ya koma Maiduguri, inda ake zargin ya ɓuya a unguwar Gomari Costain da ke ƙaramar hukumar Jere tare da taimakon wani abokinsa.

    Rundunar ta ce an kama shi ne a lokacin da ake zargin yana ƙoƙarin tsallakawa zuwa ƙasar Kamaru.

    Operation HADIN KAI ta buƙaci jama’a su ci gaba da bai wa hukumomin tsaro bayanan da suka dace domin taimakawa wajen tabbatar da zaman lafiya da tsaro a yankin Arewa maso Gabas.

  14. Iran ta ce ba za ta bar Amurka ta riƙa kai mata hari a duk lokacin da ta ga dama ba

    Iran ta ce ba za ta taɓa barin Amurka ta riƙa ƙi mata hari a duk lokacin da ta ga dama ba tana mai jaddada cewa za ta mayar da martani ga duk wani hari da za a kai mata a nan gaba.

    Kakakin ma’aikatar harkokin wajen Iran, Ismail Baghaei, ne ya bayyana haka a wani taron manema labarai, inda ya ce ƙasarsa ba za ta amince Amurka ta ƙayyade lokacin yaƙi ko zaman lafiya ba.

    Ya kuma ce halin da ake ciki yanzu ba zai iya zama abin da za a kira tsagaita wuta ba.

    Baghaei ya ƙara da cewa an samu ɗan sauƙin tashin hankali a cikin ‘yan kwanakin nan saboda dabarun rundunonin sojin Iran.

    Ya yi gargaɗin cewa duk wani sabon mataki da Amurka ta ɗauka kan Iran zai gamu da martani mai ƙarfi daga Tehran.

  15. Tinubu ya gaji, ya kamata ya yi ritaya – Peter Obi

    Dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar NDC, Peter Obi, ya buƙaci Shugaban Najeriya Bola Ahmed Tinubu ya haƙura da neman sake tsayawa takara a 2027, yana mai cewa "shugaban ya gaji kuma ba shi da karfin da zai iya magance matsalolin tattalin arziki da rashin tsaro da Najeriya ke fuskanta."

    Obi ya ce Tinubu na yanzu ba irin wanda ya yi mulkin jihar Legas ba ne a baya.

    Da yake magana a wata hira da gidan talabijin na Channels, Obi ya ce Najeriya na tafiya ne a hanya mara kyau, yana mai zargin gwamnatin Tinubu da gaza magance talauci, yunwa da rashin tsaro.

    Ya ce rahotannin ƙungiyoyin ƙasashen duniya sun nuna cewa miliyoyin 'yan Najeriya na fuskantar talauci da ƙarancin abinci, amma maimakon mayar da hankali kan waɗannan matsaloli, 'yan siyasa na tattaunawa ne kan siyasa maimakon muhimman batutuwa.

    Obi ya kuma ce "magance matsalar tsaro ba zai yiwu ba sai an rage talauci tare da zuba jari mai yawa a ilimi da samar da ayyukan yi."

    Duk da yabon da shugaban Amurka Donald Trump ya yi wa Tinubu kan kokarin tsaro, Obi ya ce abin da gwamnati ke yi a yanzu bai isa ba.

    Ya jaddada cewa burinsa ba wai zama shugaban kasa ba ne kawai, illa ganin Najeriya ta samu ci gaba da zaman lafiya.

  16. A halin yanzu ba ma tattaunawa da Amurka - Iran

    Iran ta ce a halin yanzu ba ta cikin wata tattaunawa da Amurka, inda kakakin ma’aikatar harkokin wajen ƙasar, Ismail Baghaei, ya bayyana cewa babu wata ganawa ko tattaunawa da ke gudana tsakanin ɓangarorin biyu a wannan lokaci.

    Da yake magana a taron manema labarai na yau Litinin, Baghaei ya ce rahotannin da ke cewa Iran ta nemi a zauna teburin sulhu da Amurka ba komai ba ne illa ƙoƙarin ƙirƙira labarai.

    "A yanzu babu wata tattaunawa da muke yi da Amurka," in ji shi.

    Ya ƙara da cewa a daidai lokacin da Amurka ke ci gaba da abin da ya kira tsangwama da kai wa Iran hare-hare, hankalin ƙasarsa ya karkata ne wajen kare kanta.

    Sai dai ya ce akwai yiwuwar masu shiga tsakani su isar da saƙonni daga Amurka kan halin da ake ciki a yankin.

  17. Ana fargabar gurɓacewar muhalli daga ayyukan haƙo mai a DR Congo

    Ƙungiyar kare haƙƙin bil'adama ta Human Rights Watch ta yi gargaɗin cewa ayyukan hako mai da kamfanin Perenco ke gudanarwa a yankin Muanda da ke lardin Kongo a tsakiyar Jamhuriyyar Dimokuraɗiyyar Kongo na iya zama barazana ga lafiyar al'umma da muhalli.

    Rahoton ya ce hayaƙin da kamfanin ke fitarwa da kuma ƙona tarkacen mai sun gurɓata ingancin iska, yayin da malalar mai daga rijiyoyi da bututun mai ta gurɓata koguna da ƙasa.

    Mazauna yankunan sun ce suna fama da matsalolin numfashi, ciwon ƙirji da tashin zuciya, kuma suna danganta waɗannan matsaloli da ayyukan kamfanin.

    Sai dai Perenco ya musanta zarge-zargen, yana mai cewa binciken da aka yi na da kura-kurai.

    Kamfanin ya ce ya zuba jari wajen rage gurɓacewar muhalli da kuma tallafa wa ayyukan kiwon lafiya, tare da bayyana cewa ya dakatar da fitar da hayaƙin gas a wurare sama da 200 kuma yana aiki tare da hukumomin Kongo.

    Gwamnatin Kongo, wadda ta ba da umarnin a gudanar da binciken muhalli kan ayyukan kamfanin tun ƙarshen shekarar 2024, har yanzu ba ta fitar da sakamakon binciken ba.

    Human Rights Watch na kira ga gwamnati da ta bayyana sakamakon binciken tare da ɗaukar matakan kare lafiyar jama'a.

    Perenco, wanda shi ne kaɗai kamfanin da ke samar da mai a Kongo, na gudanar da ayyuka a kan tudu da kuma a teku a bakin gaɓar ƙasar mai tsawon kilomita 37.

  18. Najeriya ta yi martani kan kisan ɗan ƙasarta a Afrika ta Kudu

    Gwamnatin Najeriya, ta hannun ofishin jakadancinta da ke Johannesburg, ta yi allawadai da kisan wani ɗan ƙasarta, Ibeh Chika Simon, wanda ya mutu a yayin wani samamen da 'yansandan Afirka ta Kudu suka kai a Bellville da ke Cape Town a ranar 23 ga Yuli.

    Jakadancin ya ce mutuwar tasa ta faru ne a yanayi mai cike da tambayoyi, yayin da kuma wani ɗan Najeriya, Egwabor Patrick Chuks, ya samu munanan raunuka bayan an harbe shi a wannan samame.

    A wata sanarwa, ofishin jakadancin ya ce ya yi matuƙar kaɗuwa da yadda lamarin ya faru, yana mai zargin jami’an tsaro da amfani da matakan da suka kai ga mutuwar marigayin.

    Haka kuma, ya bayyana lamarin a matsayin wani ɓangare na abin da ya kira ci gaba da kashe-kashen da ba a warware ba da kuma zargin cin zarafin baƙi a Afirka ta Kudu.

    Najeriya ta buƙaci hukumomin ƙasar su gudanar da bincike cikin gaggawa, adalci da gaskiya tare da hukunta duk wanda aka samu da hannu a lamarin.

    A nata ɓangaren, Kwamitin Ministoci kan Harkokin Hijira na Afirka ta Kudu ya ce ana ci gaba da binciken abin da ya faru.

    Ministar Shari’a Afrika ta Kudu, Mmamoloko Kubayi, ta ce a yayin samamen ƴansandan, wasu mutane sun yi turjiya ga jami’an tsaron yayin da kuma wasu baƙi suka hana su gudanar da aikinsu.

    Ta ce za a bayyana sakamakon binciken idan an kammala shi, tare da ƙara da cewa gwamnati na damuwa da hare-haren sintiri da ake kai wa baƙi, inda aka kama mutum bakwai da ake zargi da hannu a irin waɗannan ayyuka.

  19. Kare Lebanon shi ne sharaɗin farko a yarjejeniyar Iran da Amurka - Mojtaba

    Kafofin yaɗa labarai na Iran sun wallafa wata wasiƙa da suka ce Mojtaba Khamenei ne ya aike ta a matsayin martani ga wasiƙar shugaban Hezbollah na Lebanon da kuma mubaya’arsa gare shi.

    A cikin wasiƙar, Mojtaba Khamenei ya yabawa Hezbollah, yana mai bayyana ƙungiyar a matsayin jagorar ƙungiyoyin jihadi masu yaƙi da Isra'ila.

    Wasiƙar ta ce Iran ta ɗauki kare Hezbollah a Lebanon a matsayin wata muhimmiyar manufa ta dabarun siyasa, bisa tsarin da Ali Khamenei ya shimfiɗa.

    Haka kuma, ta bayyana cewa kiyaye cikakken ikon ƙasar Lebanon da kuma janyewar Isra'ila gaba ɗaya daga yankunanta ba tare da wani sharadi ba su ne manyan sharuɗɗan yarjejeniyar da ake son amfani da ita wajen kawo ƙarshen yaƙin Iran da Amurka.

    Rahotanni sun ce tun bayan harin da Amurka ta kai kan gidan Ayatollah Ali Khamenei da iyalansa a ranar 29 ga Maris, ba a sake ganin Mojtaba Khamenei ko jin muryarsa ba.

  20. Amurka tana ta mana tayin zaman lafiya amma kare ƙasarmu ne muraddinmu - Iran

    Kakakin Ma'aikatar Harkokin Wajen Iran, Esmail Baghaei, ya ce Amurka na ci gaba da aikewa Iran tayin sasanta rikicin da ke tsakaninsu, amma abin da Tehran ta fi bai wa muhimmanci shi ne kare ikon ƙasarta, martabarta da kuma lafiyar al'ummarta.

    Baghaei ya zargi Amurka da Isra'ila da kai hare-hare kan Iran sau biyu a baya a lokutan da ake gudanar da tattaunawa, yana mai cewa hakan ya nuna cewa an ci amanar diflomasiyya sau da dama.

    Ya kuma ce Amurka ta karya yarjejeniyar fahimtar juna da aka cimma tsakanin ɓangarorin, yayin da Shugaban Amurka Donald Trump ke zargin Iran da rashin mutunta yarjejeniyoyin da take shiga.

    Bayan kusan kwana biyu da dakatar da hare-haren ramuwar gayya tsakanin Iran da Amurka, rahotanni na nuna yiwuwar komawar ɓangarorin teburin tattaunawa domin lalubo hanyar kawo ƙarshen rikicin.