Kana amfani da shafin BBC mai bayyana rubutu kawai (babu hoto) domin rage cin data. Idan ana so a ga hotuna da bidiyo sai a koma babban shafinmu.

Koma shafi mai hoto

Samu ƙarin bayani kan shafin tattalin data

KAI TSAYE, Abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya

Wannan shafi ne na kai tsaye da ke kawo muku labaran abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya a ranar Laraba 16/09/2026

Taƙaitattu

Rahoto kai-tsaye

Nabeela Mukhtar Uba da Usman Minjibir

  1. Amurka ta sanar da taƙaita biza ga jami'an Afirka ta Kudu

    Amurka ta sanar da taƙaita bayar da takardun biza ga mutanen da ake zargi da nuna wariyar launin fata ga tsirarun farar fata a Afirka ta Kudu.

    Wannan ce taƙaddama ta baya-bayan nan tsakanin ƙasashen biyu.

    Gwamnatin Shugaba Donald Trump ta soki Afirka ta Kudu kan batutuwa da dama da suka haɗa da manufofi da aka bijiro da su don magancenuna wariya.

    Trump ya ce manufofin suna nuna wariya ga farar fata ƴan Afirka ta Kudu. Tuni dai Afirka ta Kudun ta musanta waɗannan zarge-zargen.

    Sakataren harkokin wajen Amurka, Marco Rubio ya ce gwamnatin Afirka ta Kudu ba ta warware matsalolin da ta bayyana ba, kamar yadda ya faɗa cikin wata sanarwa da ke ƙunshe da matakin.

    Ya ce taƙaita bayar da bizar za ta shafi waɗanda ke tunzura wariyar launin fata.

    Sai dai Rubio bai fito ya bayyana sunan waɗanda matakin ya shafa ba.

  2. ADC ta zargi Tinubu da jefa ƴan Najeriya cikin halin ha'ula'i

    Jam'iyyar hamayya ta African Democratic Congress (ADC) ta zargi gwamnatin Shugaba Bola Tinubu da taɓarɓara tattalin arzikin ƙasar sakamakon tashin farashin mai da ya kai har ₦1,470 kowace lita.

    Jam'iyyar ta ce tashin farashin man ya janyo ƙaruwar farashin sufuri da abubuwan yau da kullum, lamarin kuma da ya ƙara jefa ƴan Najeriya cikin mawuyacin yanayi.

    A cewar Gidan Talabijin na Channels, wata sanarwa da Sakataren Yaɗa Labaran ADC, Bolaji Abdullahi, jam'iyyar ta ce ana jin raɗaɗin tasirin tashin farashin man har a kayan masarufi da sufuri da wutar lantarki da ilimi da sauran ɓangarorin rayuwa.

    "Shugaba Tinubu ya mayar da batun man fetur wani makamin gallazawa ga ƴan Najeriya. Kayan masarufi, sufuri, lantarki, ilimi da duk abubuwan da ƴan Najeriya ke nema don ci gaba da rayuwa na da alaƙa da farashin mai," in ji jam'iyyar.

    ADC ta kuma bayyana wasu rahotanni na makarantun kuɗi da suka ƙara kuɗin makaranta da kashi 30 zuwa 40, inda jam'iyyar ta ce hakan ya ƙara nuna yadda taɓarɓarewar tattalin arzikin ƙasar ya yi ƙamari.

  3. Ɓarnar da Iran ta yi wa sansanonin sojin Amurka a Gabas ta Tsakiya

    Kafar yaɗa labarai ta CBS ta saki wasu sabbin hotuna da ke nuna irin ɓarnar da aka yi wa gine-gine da motoci a sansanonin sojin Amurka da ke Gabas ta Tsakiya bayan da hare-haren makamai masu linzami da na jirage marasa matuƙa da Iran ta kai.

    Sojoji ne suka aikewa kafar ta CBS inda suka nemi a saka sunansu kasancewar akwai takunkumi kan yaɗa labarai a rundunar sojin Amurka.

    Ɗaya daga cikin hotunan da CBS ta samu daga sansanin sojoji na Prince Sultan a Saudiyya sun nuna yadda harin ya shafi bayan injin jirgi ƙirar Being A-3.

  4. Fitaccen jarumin Nollywood Olu Jacob ya mutu

    Iyalan ɗaya daga cikin fitattun ƴan fim a masana'antar fina-finai ta Nollywood, Olu Jacob sun sanar da rasuwarsa yana da shekara 84.

    Sun yi sanarwar ne da safiyar yau Laraba inda suka nemi jama'a da su yi wa mamacin addu'a.

    An jima rabon da a ga Olu Jacobs a bainar jama'a kuma a 2021 ne mai ɗakinsa Joke Silva, wadda ita ma fitacciyar ƴar Nollywood ce - ta bayyana cewa an gano mijin nata na ɗauke da cutar mantuwa.

    Cuta ce da ke shafar ƙwaƙwalwa da lafiyar mutum, kamar yadda mai ɗakin nasa ta faɗa a wata hira da ɗan jarida Chude Jideonwo.

    Lokuta da dama a baya, an sha yaɗa labarin mutuwarsa amma iyalansa suka gaggauta ƙaryatawa, inda ko a shekarar 2024 ma sai da babban ɗansa Soji ya yi jawabi a talabijin don ya ƙaryata jita-jitar.

    Marigayin ya soma harkar fim ne a Birtaniya a shekarun 1970 inda ya haska a fina-finai kamar The Goodies, Till Death Do Us Part, Angels and The Tomorrow People.

  5. Mutum 12 sun mutu bayan ruftawar ginin a yaƙi ya shafa a Gaza

    Aƙalla mutum 12 aka kashe har da ƙananan yara sannan wasu gommai sun yi ɓatan dabo bayan da wani rukunin gidaje ya rufa a zirin Gaza.

    Jami'an ceto sun duƙufa wajen zaƙulo gawarwaki da kuma mutanen da ke da sauran numfashi waɗanda suka maƙale ƙarƙashin ɓuraguzai.

    Rahotanni sun ce mutanen da yaƙin Isra'ila ya shafa ne ke zama a gidan mai hawa shida da ke yankin Tal al-Hawa, a kudu maso yammacin Gaza.

    Hukumar tsaro ta bayyana cewa ta samu damar aro wasu manyan kayan aiki don taimakawa a ayyukan ceto.

    Isra’ila ta ƙaƙaba takunkumi masu tsauri kan kayan aikin da za a iya shigar da su Gaza.

  6. Houthi ta musanta kai harin jirgi mara matuƙi kan Makkah

    Mayaƙan Houthi a Yemen sun ce sun harbo wani jirgin yaƙin Saudiyya a Lardin Marib.

    Sai dai zuwa yanzu BBC ba ta iya tantace wannan iƙirarin ba amma wani kakakin Houthi ya zargi Saudiyya da ƙaddamar da hare-hare kan Yemen ciki har da ɗaruruwan hare-hare da ta kai jiya.

    Ƙungiyar ta kuma musanta iƙirarin Saudiyya cewa ta kai hari zuwa Makka ta hanyar amfani da jirgi mara matuƙi inda ta ce ta kai harin ne kan wasu cibiyoyin mai da wuraren sojoji da ke nesa da birnin na Makkah.

    Saudiyya dai ta ce ta harbo jirgin.

  7. 'Ya kamata duniya ta aminta da kamfanonin AI'

    Shugaban kamfanin OpenAI ya ce ya kamata duniya ta amince cewa kamfaninsa na yin abin da ya kamata duk da ci gaba da nuna damuwa da ake a kan bunƙasa kirkirarriyar basira cikin gaggawa.

    Babban jami’in kamfanin, Sam Altman, ya ce samfurorin kirkirarriyar basirar sun kai wani matsayi da ke buƙatar a sake tsara yadda ake tafiyar da su.

    Wakiliyar BBC ta ce Sam Altman ya ce ya kamata kamfaninsu na Open AI da sauran kamfanonin kirkirarriyar basira su rika yin abubuwa a bude, sannan kuma su rika kai rahoton duk wata matsala ta kirkirarriyar basira idan an samu.

    A watannin baya-bayan nan, an samu rahotannin cewa wasu nau'ikan kirkirarriyar basirar sun tsallake wani gwaji da aka yi tare da ƙoƙarin kutse cikin tsarin wasu kamfanoni, lamarin da ya sa wasu masu bincike ke gargadin cewa irin wadannan kirkirarrun basirar na iya zama barazana ga bil’adama.

  8. Saudiyya ta zargi mayaƙan Houthi da kai hari Makkah

    Rundunar sojin Saudiya ta ce ta harbo wani jirgin sama marar matuƙi da ke kan hanyarsa ta zuwa birnin Makka.

    Wakiliyar BBC ta ce mai magana da yawun gwamatin Saudiyyan ya ce an lalata jirgi marar matukin ne a yammacin jiya Talata a kudancin birnin Makka lamarin da ya ce matakin ya kai abin da ba za a iya amincewa da shi ba.

    Mahukuntan ƙasar sun zargi mayaƙan Houthi da kai harin. Ƙungiyar Haɗin Kan Kasashen Musulmi ta OIC, ta yi tur da abin da ta bayyana a matsayin “mummunan hari” da Houthi ta kai, sai dai ƙungiyar mai samun goyon bayan Iran ta musanta hannu a lamarin.

    Rikicin da kuma barazanar da yake yi ga zirga-zirgar jiragen ruwa na daga cikin batutuwan da Kwamitin Sulhu na Majalisar Ɗinkin Duniya ya tattauna a wani taron gaggawa da ya gudanar a jiya Talata.

  9. Assalamu Alaikum!

    Barkan ku da zuwa shafin Kai Tsaye na BBC Hausa da ke kawo muku labarai na abubuwan da ke faruwa a Najeriya da ma sauran sassan duniya.

    Sai ku kasance tare da mu a wannan rana ta Laraba don sanin halin da ƙasashen duniya ke ciki.

    Sunana Nabeela Mukhtar Uba kuma zan kasance da ku har zuwa anjima da abokan aiki za su karɓi ragama.

    Kuna iya leƙawa shafukanmu na sada zumunta domin samun ƙarin labarai har ma da kallon bidiyo.