Za mu lalata jiragen dakon man fetur ɗin Iran - Amurka

Asalin hoton, Getty Images
Sakataren Tsaron Amurka ya yi barazanar cewa idan Iran ta kai wa jiragen ruwan Amurka hari, Amurka za ta mayar da martani ta hanyar “lalata tare da nutsar da jiragen dakon man fetur ɗinta.”
Pete Hegseth ya wallafa a shafin X, yana magana kan sabon sanarwar Rundunar Sojin Amurka da ke kula da yankin Gabas ta Tsakiya (CENTCOM), cewa: “Abu ne mai sauƙi: Idan Iran ta kai wa jiragen ruwan Amurka hari, za mu lalata (tare da nutsar da) jiragen dakon man fetur ɗinta.”
A cewarsa, abin da Iran ke bukata kawai shi ne “kada ta kai wa Rundunar Sojin Ruwa ta Amurka hari.”
Mista Hegseth ya ce: “Rundunar jiragen dakon man fetur ta Iran ba ta da kariya. Iran ba ta da rundunar sojin ruwa ko ta sama. Jiragen samanmu, jiragen ruwanmu da kuma jiragen ruwa masu tafiya ƙarƙashin ruwa na iya kai musu hari gaba ɗaya.”
Sa’o’i kaɗan da suka gabata, CENTCOM ta ce ta kai hari kan jiragen dakon man fetur uku na Iran, yayin da Admiral Brad Cooper, kwamandan CENTCOM, ya aika da saƙo cewa: “Saƙon da muke son ya isa ga IRGC ya zama a bayyane: Idan kuka yi wa biyu daga cikin jiragen ruwanmu hari, za mu jefa muku wani ƙarin tsadar tattalin arziki; wato, za mu lalata jiragen ruwanku uku.”




















