KAI TSAYE, Abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sassan duniya

Wannan shafi ne na kai tsaye da ke kawo muku labaran al'amuran da ke faruwa a Najeriya da sassan duniya na ranar 05/09/2026.

Tsallake Bidiyo ka ci gaba
  • Adeyemi Adeniyi
  • Abdourahamane Tchiani
  • Atiku Abubakar
  • NFF
  • Badriyyah Tijjani Kalarawi
  • Ranar Hausa: BBC
  • Danjuma Goje
  • Zainab
  • BBC
  • ABU
  • xxx
  • xxx
  • Khalifa Dokaji
  • Sheikh Jingir
  • Kano

Rahoto kai-tsaye

Isiyaku Muhammed

  1. Hare-haren Isra'ila sun kashe mutum uku da jikkata 20 a Lebanon

    Netanyahu

    Asalin hoton, Reuters

    Ma’aikatar Lafiya ta Lebanon ta ce mutum uku sun mutu yayin da wasu fiye da mutum 20 kuma suka jikkata sakamakon hare-haren da Isra’ila ta kai a kudanci da gabashin ƙasar.

    Sojojin Isra’ila sun ce sun kai hare-haren ne a matsayin martanin wani harin jirgin sama marar matuki da ƙungiyar Hezbollah ta kai kan sojojinsu da ke Lebanon.

    Isra’ila na ci gaba da kasancewa da sojojinta a wasu yankuna na kudancin Lebanon tun bayan kaddamar da wani gagarumin farmaki kan Hezbollah a watan Maris, bayan da ƙungiyar ta kai hari da jirage marasa matuƙa zuwa Isra’ila domin nuna goyon baya ga Iran.

    Duk da yarjejeniyar tsagaita wuta da Amurka ta taimaka wajen kulla wa, Isra’ila da Hezbollah na ci gaba da kai wa juna hare-hare akai-akai a cikin ƙasar Lebanon.

  2. Amurka za ta sayar wa Saudiyya makamai na dala biliyan 5

    Amurka da Saudi

    Asalin hoton, Getty Images

    Ma’aikatar Harkokin Wajen Amurka ta sanar da amincewa da wata yarjejeniya ta sayar wa Saudiyya kayan makamai da darajarsu ta kai dala biliyan 5.

    A cikin wata sanarwa, Ma’aikatar Harkokin Wajen Amurka ta ce ta amince da buƙatar Saudiyya na sayen dubban bama-bamai da kuma na’urorin jagorantar makamai masu linzami masu dogon zango.

    A cewar ma’aikatar, ban da makaman, yarjejeniyar za ta haɗa da manyan makamai da kayayyakin gyara da sinadarai da kuma ayyukan tallafin fasaha da dabarun sufuri da samar da kayayyaki.

    Amurka ta bayyana yarjejeniyar a matsayin wani mataki na inganta tsaron wata muhimmiyar ƙawarta, tare da taimakawa wajen tabbatar da zaman lafiyar siyasa da ci gaban tattalin arziki a yankin Tekun Fasha.

    Sanarwar ta kuma jaddada cewa yarjejeniyar za ta taimaka wajen ƙarfafa ƙarfin tsaron sararin samaniyar Saudiyya domin fuskantar barazanar da ake samu a yankin a halin yanzu.

  3. Buɗewa

    Masu bibiyarmu barka da safiyar ranar Asabar daga nan sashen Hausa na BBC.

    Yau ma mun dawo kamar kullum da labarai da rahotanni da sharhi kan muhimman abubuwan da ke faruwa a Najeriya da Nijar da sauran sassan duniya.

    Da fatan za ku ci gaba da kasance da wannan shafi na kai tsaye na sashen Hausa na BBC. Ka da ku manta za ku iya leƙawa sauran shafukan namu na sada zumunta domin samun ƙarin labarai da rahotanni da ma hirarraki.