Hare-haren Isra'ila sun kashe mutum uku da jikkata 20 a Lebanon

Asalin hoton, Reuters
Ma’aikatar Lafiya ta Lebanon ta ce mutum uku sun mutu yayin da wasu fiye da mutum 20 kuma suka jikkata sakamakon hare-haren da Isra’ila ta kai a kudanci da gabashin ƙasar.
Sojojin Isra’ila sun ce sun kai hare-haren ne a matsayin martanin wani harin jirgin sama marar matuki da ƙungiyar Hezbollah ta kai kan sojojinsu da ke Lebanon.
Isra’ila na ci gaba da kasancewa da sojojinta a wasu yankuna na kudancin Lebanon tun bayan kaddamar da wani gagarumin farmaki kan Hezbollah a watan Maris, bayan da ƙungiyar ta kai hari da jirage marasa matuƙa zuwa Isra’ila domin nuna goyon baya ga Iran.
Duk da yarjejeniyar tsagaita wuta da Amurka ta taimaka wajen kulla wa, Isra’ila da Hezbollah na ci gaba da kai wa juna hare-hare akai-akai a cikin ƙasar Lebanon.
















