Ghana ta kama aƙalla baƙin haure 600, ciki har da ƙananan yara 400

Asalin hoton, Getty Images
Hukumomin ƙasar Ghana sun kama sama da mutum 600 ƴan ci-rani da ba su da takardun izinin zama, a birni na biyu mafi girma a ƙasar, wato Kumasi.
Rahotanni sun ce daga cikin waɗanda aka tsare akwai kusan yara 400 da kuma mata 72. Hukumomin Ghana sun ce samamen wani ɓangare ne na wani shiri da ke nufin ƙaƙƙabe mabarata ‘yan ƙasashen waje da ke taruwa a cikin biranen ƙasar.
Ana ci gaba da tantance waɗanda aka kama domin gano ƙasashensu da kuma duba ko su ne waɗanda ake safarar su da masu ɗaukar nauyin su.















