Ƴansanda sun yi gargaɗi game da harin martani kan ƴan Afirka ta Kudu
Ƴansanda a Najeriya sun yi gargaɗi kan kai hare-haren ramuwar gayya kan ƴan Afirka ta Kudu ko ma wuraren kasuwancinsu sakamakon zanga-zangar ƙin jinin baƙi da ake yi a Afirka ta Kudun.
Ƴansanda sun buƙaci ƴan Najeriya da kada su ɗauki doka a hannunsu bayan "rahotannin hare-hare kan ƴan Najeriya a Afirka ta Kudu".
Ba a samu rahoton faruwar irin hare-haren ba amma gargaɗin na zuwa ne bayan wani taron manyan jami'an tsaro.
Ƴansandan Afirka ta Kudu ba su tabbatar da hare-hare kan baƙi ba duk da cewa gwamnati ta yi allawaai da miyagun laifukan da ake aikatawa kan baƙi.
A baya-bayan nan ana ta zaman ɗar-ɗar a Afirka ta Kudu sakamakon zanga-zangar neman a tsaurara matakai kan baƙin haure.
Ƙasashen Afirka da dama sun shawarci al'umominsu da su kasance cikin shirin ko ta kwana, inda a baya-bayan nan Ghana ta kwashe ɗaruruwan ƴan ƙasarta saboda tabbatar da tsaronsu.