KAI TSAYE, Abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya, Alhamis 16/07/2026

Wannan shafi ne da ke kawo muku labaran abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya, Alhamis 16/07/2026

Taƙaitattu

Skip Bidiyo and continue reading
  • Zahra Buhari
  • xxx
  • Nigeria
  • xxx
  • Davido
  • xxx
  • Zanga-zanga a aAfirka ta Kudu
  • xxx
  • Ummulkhairi Aliyu
  • xxx
  • xxx
  • xxx
  • xxx
  • Arsenal

Rahoto kai-tsaye

Abdullahi Bello Diginza

  1. Iran ta ce ta kakkaɓo jirgin Amurka maras matuƙi

    jirgi maras matuƙi

    Asalin hoton, EPA

    Iran ta ce ta kakkaɓo jirgin Amurka maras matuƙi samfurin MQ-9, wanda ta ce yana shawagi a saman birnin Andimeshk.

    A cewar dakarun juyin juya halin ƙasar, an kakkaɓo da jirgin ta hanyar amfani da sabbin makamanta na tsaron sararin samaniya.

    Kamfanin dillancin labarai na Tasnim mai alaƙa da rundunar juyin juya halin ƙasar, ya ce aikin kakkaɓo da jirgin ya yi nasara, amma bai bayar da shaidar da za ta tabbatar da iƙirarin ba.

    Kawo yanzu gwamnatin Amurka da rundunar sojin ƙasar ta CENTCOM, ba su tabbatar da iƙirarin ba.

  2. Amurka da amince da sayar wa Saudiyya da Kuwait makamai

    Makamai

    Asalin hoton, ..

    Ma'aikatar harkokin wajen Amurka ta amince da sayar wa Saudiyya makamai na kusan dala biliyan 1.96 domin ƙarfafa tsarin kariyar sararin samaniyar ƙasar.

    Matakin na zuwa ne a daidai lokacin da rikice-rikice ke ƙara kamari a yankin Gabas ta Tsakiya.

    "Sayar da ya samu goyon bayan manufofin harkokin wajen Amurka da kuma muradun tsaronta ta hanyar ƙarfafa tsaron wata muhimmiyar ƙawa da ba mambar ƙungiyar NATO ba''.

    ''Saudiyya na taka muhimmiyar rawa wajen tabbatar da zaman lafiya da bunƙasar tattalin arziki a yankin Tekun Fasha." a cewar sanarwar ma'aikatar wajen Amurkan.

    Ma'aikatar ta kuma bayyana cewa yarjejeniyar sayar da makaman ta ƙunshi na'urorin sarrafa makamai masu linzami har 20,000, waɗanda za a yi amfani da su wajen hare-hare ta sama da ta ƙasa.

    Yarjejeniyar ta kuma haɗa da na'urorin harba makamai da bama-bamai da kayayyakin gyara da horaswa da kuma tallafin dabaru da sufuri.

    Haka kuma ma'aikatar harkokin wajen Amurkan ta amince da wani ƙunshin tallafi daban na dala miliyan 484 ga Kuwait domin tallafin fasaha ga jiragen sama.

    Ana sa ran kammala da aiwatar da waɗannan yarjejeniyoyin bayan majalisar dokokin Amurka ta yi nazari tare da amincewa da su.

  3. Mun kai hari kan sadarwar Amurka da tankokin mai a Jordan - Iran

    Kafofin yaɗa labaran Amurka sun ambato rundunar sojin ƙasar na cewa sun kai hari kan cibiyar sadarwar Amurka da wasu tankokin mai na sojojin Amurka a Jordan.

    Kamfanin dillancin labarai na Tasnim ya ce ''Iran ta yi amfani da jirage marasa matuƙa na yaƙi wajen ƙaddamar da hare-haren cikin dare a sansanin sojin Amurka na Al-Azraq da ke Jordan''.

    ''A wannan sansanin ne aka girke na'urorin kakkaɓo makaman linzami, kuma ana kallaonsa a matsayin ɗaya daga cikin cibiyoyi mafiya muhimmanci ga Amurka da yankin Yammacin Asiya'', kamar yadda Tasnim ya rubuta.

  4. Pakistan ta yi kira ga Iran da Amurka su koma teburin sulhu

    Wakilan Pakistan ta Iran

    Asalin hoton, Getty Images

    Ƙasar Pakistan ta ce ta yi kira ga Amurka da Iran su dakatar da yaƙin da ke tsakaninsu tare da komawa teburin tattaunawa domin gyara yarjejeniyar da aka cimma a watan da ya gabata.

    Kakakin ma'aikatar harkokin wajen Pakistan, Tahir Andrabi ya ce duk da ƙalubalen da aka samu wajen aiki da yarjejeniyar, Pakistan za ta ci gaba da ƙarfafa ɓangarorin biyu don kawo ƙarshen rikicin.

    ''Muna fatan halin da ake ciki kan mashigar Hormuz zai daidaita nan ba da jimawa ba''.

    Ya ƙara jaddada muhimmancin mashigar tare da ci gaba da tsareta da samar da ƴancin walwala ga jiragen da ke bi da wurin.

    A wannan makon ne Amurka da ƙaddamar da hare-hare kan Iran, yayin da ita ma tehran ta mayar da martani wajen kai wa sansanonin sojin Amurka hare-hare a yankin Gulf.

  5. 'An kashe wani babban injiniya Zaporizhzhia'

    Kamfanin makamashin nukiliya na gwamnatin Rasha ya ce an kashe babban injiniyan tashar samar da wutar lantarki ta nukiliya a yankin Zaporizhzhia, da ke Ukraine, wadda Rasha ke iko da ita, a harin da wani jirgin mara matuƙi na ƙasar Ukraine ya kai kusa da tashar.

    Hukumar Kula da Makamashin Nukiliya ta Duniya (IAEA) ta ce an sanar da ita game da mutuwar jami'in, tare da sake nanata kiranta da a dakatar da duk wani hari da ake kai wa kusa da cibiyoyin nukiliya da ma'aikatansu.

    Sojojin Rasha sun ƙwace iko da tashar Zapo-rijiya ne a makonnin farko na mamayar da Moscow ta ƙaddamar kan Ukraine a shekarar 2022.

    A wani labarin kuma, Rasha ta sake kai wa Kyiv babban birnin Ukraine, hare-haren makamai masu linzami , inda aka ba da rahoton fashe-fashe da dama a safiyar yau Alhamis.

  6. An ji ƙarar sabbin fashewa a Iran

    sojoji

    Asalin hoton, ..

    An ji ƙarar fashewar abubuwa a sassa daban-daban na Iran, ciki har da yankunan da ke nesa da Tekun Fasha, yayin da rundunar sojin Amurka ta sanar cewa ta ƙaddamar da wani sabon zagayen hare-hare.

    A babban birnin ƙasar, Tehran, an yi amfani da na'urar kakkaɓo makamai masu linzami yayin da a birnin Ah-vaz da ke kusa da arewacin Tekun Fasha.

    Kafafen yaɗa labaran ƙasar sun ce an kwashe marasa lafiya daga wani asibiti saboda hare-haren makamai masu linzami da aka kai a kusa da yankin.

    Babban mai shiga tsakani na Iran a tattaunawarta da Amurka, Mohammed Bagher Qalibaf, ya fitar da wata sanarwa yana mai cewa ƙasarsa na ci gaba da bin tafarkin tattaunawa da kuma yaƙi a lokaci guda, amma ya zama dole Iran ta ci gaba da riƙe ikon kula da mashigin ruwan Hormuz.

    Iran ta mayar da martani tana mai cewa ta mayar da hankali ne wajen lalata cibiyoyin sojin Amurka da ke yankin Gabas ta Tsakiya.

  7. Assalamu alaikum

    Masu bin shafin BBC Hausa barkanmu da safiyar wannan rana ta Alhamis.

    Abdullahi Bello Diginza ke fatan sake kasancewa da ku a daidai wannan lokacin domin kawo muku halin da duniya ke ciki.

    Ku biyo mu a shafukanmu na sada zumunta domin tafka muhawara kan labaran da muek wallafawa