Hezbollah ta ce ta yi artabu da sojojin Isra’ila a Kudancin Lebanon
Ƙungiyar Hezbollah ta sanar da cewa dakarunta sun yi arangama da sojojin Isra’ila da ke ƙoƙarin isa garin Majdal Zun da ke kudancin Lebanon.
Ta ce ta harba roƙoƙi kan sojojin Isra’ila a ranar Alhamis, lamarin da ya tilasta musu ja da baya.
A wata sanarwa da ta fitar, ƙungiyar ta ƙara da cewa a ranar Juma’a ta sake kai hare-hare da makamai masu linzami da kuma roƙoƙi.
Har ila yau, ta ce ta kai wasu ƙarin hare-hare kan sojojin Isra’ila a yankunan kudancin ƙasar.
A ɓangare guda, sojojin Isra’ila sun buƙaci mazauna wasu ƙauyuka uku a kudancin Lebanon da su bar gidajensu, yayin da rahotanni suka ce ana ci gaba da kai hare-hare a yankuna daban-daban.
Hukumomin labaran Lebanon sun kuma ruwaito ƙararrakin fashe-fashe masu ƙarfi da harba makamai a kusa da yankin Ali Taher.