Brazil ta hana ƴan Amurka masu sa ido kan zaɓe bizar shiga ƙasar
Wasu rahotanni sun ce Brazil ta ƙi ba wasu jami'an Amurka biyu biza, waɗanda suka shirya zuwa kasar domin duba aka shirya yin zaben kasar wanda za a yi a watan Oktoba.
Majiyoyin diflomasiyya sun ce jami'an na son nuna shakku kan sahihancin tsarin zaɓen Brazil, zargin da Amurka ta musanta zargin, inda ta bayyana shi a matsayin "ƙarya marar tushe".
A zaɓen da ke tafe, Shugaba Luiz Inácio Lula da Silva (Lula) zai fafata da Flavio Bolsonaro, wanda jam'iyyar Liberal mai ra'ayin mazan jiya ta amince da shi a hukumance a matsayin ɗan takararta a ranar Asabar.
Flavio Bolsonaro na daga cikin abokan siyasar Shugaban Amurka Donald Trump, kuma ya sha bayyana shakkunsa kan amincin tsarin zaɓen da ake yi ta hanyar na'urar kwamfuta a Brazil din.
Mahaifinsa, tsohon shugaban ƙasar Jair Bolsonaro, na zaman hukuncin daurin kurkuku bayan an same shi da laifin shirya wani yunkurin juyin mulki, kamar yadda rahotanni suka bayyana.