Qatar ta ce tana 'ƙoƙarin sake dawo da tattaunawa' tsakanin Iran da Amurka
Kakakin ma'aikatar harkokin wajen Qatar ya sanar da cewa tana aiki "tare da abokan hulɗarta a yankin da ma sauran sassan duniya, ciki har da China," domin sake fara tattaunawa tsakanin Amurka da Iran.
A halin yanzu, Firaminista kuma Ministan harkokin wajen Qatar ne ke jagorantar tawagar da ta tafi birnin Beijing.
A cewar Jamhuriyar Musulunci ta Iran, Pakistan ce babbar mai shiga tsakani tsakanin Iran da Amurka a halin yanzu, amma jami'an Qatar ma suna taka rawa sosai a wannan aiki na shiga tsakani.
An samu rahoton cewa, kwanan nan wata tawagar jami'an diflomasiyyar Qatar ta ziyarci Iran.
A jiya ne kakakin ma'aikatar harkokin wajen Iran ya bayyana cewa, tawagar ta gana da Ministan harkokin waje Abbas Araqchi, inda aka bayyana cewa manufar ziyarar ita ce "ci gaba da ƙoƙarin rage tashin hankali" a yankin.