Iran ta ce sake buɗe intanet ga jama'a mataki ne na kare haƙƙoƙinsu
Mai magana da yawun gwamnatin Iran, Fatemeh Mohajerani, ta bayyana cewa matakin da gwamnati ta ɗauka na sake buɗe intanet na duniya ga jama'a ba kawai cire wata takunkumin fasaha ba ne, illa wani mataki ne na tabbatar da haƙƙoƙin al'umma.
A cikin wata sanarwa da ta fitar, Mohajerani ta ce katse intanet din da aka yi a watannin baya ya samo asali ne daga barazanar tsaro da hare-haren abokan gaba da kuma yanayin da ya biyo bayan hakan.
Ta ƙara da cewa kundin tsarin mulkin ƙasar ya tanadi cewa babu wani yanayi na musamman da zai zama dindindin.
Bayan shafe watanni ana fama da katsewar intanet a Iran sakamakon yaƙin da ya ɓarke tsakanin Iran da Amurka da Isra'ila, an fara mayar da wasu ayyukan intanet a ƙasar kwanaki biyu da suka gabata.
Tun da farko, gwamnatin Shugaba Masoud Pezeshkian ta yi kira sau da dama da a dawo da intanet, tana mai gargadin cewa katsewar na haifar da illa ga harkokin ilimi, tattalin arziki da kuma kasuwanci a ƙasar.