A gargaɗi ƴan Zambiya kan cin mushen dabbobi sakamakon cutar anthrax
Hukumomi a Zambiya sun gargaɗi ƴan ƙasar da su guji cin naman dabbobin daji bayan da dabbobi da dama suka mutu sakamakon cutar anthrax.
Wani jami'i na hukumar kare afkuwar bala'i ya ce a ƙarshen makon da ya gabata, mutum 12 ne suka kamu da cutar bayan da suka ci naman dabbobin a yankin kogin Munyamadzi.
Jami'in ya yi kira ga jama'a da su guji cin naman dabbobin da ba a tantance dalilin mutuwarsu ba.
Zuwa yanzu jami'ai ba su tantance girman ɓarkewar cutar a baya-bayan nan ba inda ake ci gaba da sa ido da kuma gwaji a ɗakin gwaje-gwaje.
A shekarar 2023, ƙasar ta yi fama da ɓarkewar cutar da ba a yi tunani ba, har ta kai mutum huɗu sun mutu sannan kuma ta bazu zuwa larduna tara cikin 10.