Hare-haren Isra'ila a Lebanon sun yi sanadiyyar mutuwar mutum 110 cikin kwanaki 5
Ma'aikatar lafiya ta ƙasar Lebanon ta ce hare-haren da Isra'ila ta kai sun yi sanadiyar mutuwar mutane dari da goma tun daga ranar Alhamis, duk da yarjejeniyar tsagaita wuta da aka cimma sama da makonni biyu da suka gabata.
Ranar litinin na daya daga cikin ranaku mafi muni a ‘yan kwanakin nan, inda sojojin Isra’ila suka kashe mutane goma sha bakwai da suka hada da kananan yara biyu.
Wakilin BBC ya ce A kudancin Lebanon, wannan tsagaita wuta a suna ne kawai, Isra'ila ta ci gaba da kai hare-hare ta sama a kowace rana.
Isra'ila dai ta dage kan cewa kungiyar Hezbullah ta ke kai wa hari.
Kamfanin dillancin labaran kasar Lebanon ya ruwaito cewa, sojojin kasar Isra’ila sun kai hare-hare ta sama kan wasu wurare sama da ashirin a kudancin kasar ta Lebanon a jiya litinin